FARAR HAIHUWA💰1
Bismillahir Rahmanir Rahim
Kai kawo take tayi a siririn corridor din asibitin cikin tsananin tashin hankalin rashin sanin halin da kanwarta take ciki. Inna Uwale dake zaune a kan tabarma ta daga hannu sama idanunta duk sun ciko da hawaye tace Ya Allah ka bani farin jika ko wanne iri ne. Ya Allah fari kyakkyawa kamar ni. Zulai aminiyarta tace amin amin Uwale ai ranar sai munyi sadaka. Tani dake kai kawo da sauran matan da 'yan uwansu ke cikin dakin haihuwar suka zuba mata ido. Ta kuwa cigaba da adduar farin jika kamar yadda ta saba. Cikin kunar rai Tani tace amma Uwale baki da mutumci ko kadan. Kanwar tawa tana ciki rai a hannun Allah kina wani fatan a haifa miki farin jika. Farin jikan yaci.....bullowar mal Yakubu yasa tayi shiru ta share hawayen bakin cikin da ke shirin sauko mata. Ita kuwa Inna Uwale tace ashe baki da kunya Tani? Ban girmi uwarki Baraatu ba? Ita dai Tani shiru tayi don tana gani mutumcin Mal Yakubu mijin kanwarta. Yayi gumi sharkaf saboda tafiyar da yayi zuwa asibitin a kafa bayan dan Tani din ya bishi gona ya sanar dashi halin da ake ciki. Ramlah da Sadi suna ganinsa suka mike suna murna suka tsaya a gabansa. Daukar Sadi yayi itama Ramlah tasa kuka sai an dauketa. Tana kukan bata sani ba ta taka kafar Inna Uwale. Wata kara ta saki kafin ta hankade ta ta fadi kasa. Matsa can gun yar uwarki, shegiya baka mummuna. Mal Yakubu yace haba inna a nan din ma. Tani ta dauke ta tana goge mata bakinta da yasha kasa. Yarinya sai kuka take. Yo ba kaine duk ka cuceni ba dan nan. Mata aka sami abin kallo jin yadda Uwale ta bude murya. Ta cigaba dube ni nan ga fari ga kyau haka Allah Yayi ni tun kuruciya don ma girma yazo. Ta daga siririyar kafarta ta hagu wadda shan inna ya shanye tace da wannan Allah Ya ragewa aya zakinta duk kyan dire na ban sami mijin arziki ba sai ubanka. Allah dai Ya jikansa. Babu irin adduar da banyi ba da cikin ka don ka fini sanin baki ne. Allah Ya taimake ni na haifo ka fari tas ga kyau. Sai hawaye shar suka sauko mata ya durkusa kasa don Allah Inna kiyi shiru. Sauran matan dake wurin suna ta kallo an sami labarin kaiwa gida yau. Yaron nan da yake mai bakin kashi ne ya rasa wadda zai aura sai yar maiduguri. Wallahi kunga wannan yayar tata ta nuna Tani har ta fita haske. Kalarta fa kamar dauda yadda dai kuka ga 'ya'yan nan. Ba yadda banyi ba har da kwanciya a asibiti duk don a fasa auren yaki jin maganata. Ga haihuwar balai duk shekara. Yanzu wannan cakurkurar, ta nuna Ramlah zaayiwa kani na biyu. To ni mijina ba arziki har ya mutu shima dan babu. Ni kuwa kafin na mutu sai naje makka da kudin jika ko na mijin jika. Haka kawai yadda nake da kyan nan bazan bar baya bakikkirin ba. Mal Yakubu ya share hawayen idanunsa. Inda sabo ya saba da halin innarsa amma irin wannan a cikin mutane ta gama zubar masa da mutumci.
Goron bakinta ta furzar tace wallahi indai ta haifi fari ko fara nayi alqawarin yi mata wankan jego da hannuna. Ga mutane suna min shaida. Ni ban tsani Munari ba harkar bakar fata ahalin tsiya da talauci ne bana so. Tana gama magana wata nurse ta fito tace ina wadanda suka kawo Maimunatu Ado? Mal Yakubu yayi saurin matsowa gaba. Inna uwale ma ta cangalo kafa tace Nas fada min me aka samu. Fari ne? Ko kallonta nurse din bata yi ba tace masa ta sauka lafiya za'a fito da ita zuwa dakin hutu. Uwale tace tana zaro manyan idanunta ke yar nan karki min rashin kunya, ya ina tambayarki me aka samu zaki min banza. Ki fada min gaskiya fari ne ko baki? Don wadan can yaran ko irin farin nan na jarirai wallahi baa haifesu dashi ba. Nurse ta kalli mal Yakubu tace masa namiji ne tayi gaba abinta.
Zulai kawar uwale ta kama hanci ta rangada guda. Uwale ta kuwa make ta, to uwar kinibibi ai baki ga kalar dan ba zaki cika mana kunne.
Batul Mamman💖
FARAR HAIHUWA💰2
Da dafa bango Munari ta fito daga dakin nurse na biye da ita da jaririn. Tani ta gyara goyonta ta mika hannu zata karbi dan Uwale tayi saurin shigewa gabanta tace bani nan. Ni na haifi ubansa. Tana bude zani ta kwala ihu ta mikawa zulai dan ta kai goshinta kasa tayi sujjada. Allah nagode maka...ta kalli surukarta munari kin kwaci kanki wallahi. Ke dai Allah Yayi miki albarka. Da kanta ta rike Munari suka karasa dakin aka bata gado. Tani da mijinta suna ta yi mata sannu. Inna uwale ta sake karbar dan tana ta washe baki tace jamaa kunga abin arziki ko. Yarinya mai son gamawa da duniya lafiya kenan. Ashe tumatir da su mangwaron dana rinka siya miki yau kinga ranarsu ko. Ashe banyi asarar kudina ba. Zulai ai na fada miki duk miyar kadi ko harkar daddawa sai da na hanata gashi kuwa kwalliya ta biya kudin sabulu. Kiri kiri ta hana kowa daukarsa saboda tsabar murna. Zaninta taji zai kwance ta mikawa Zulai dan ba don taso ba tana magana. Ai sunan babana zaa saka maka yaro. Nima a nan na gado farin da kyau har kaima ka dandala. Zulai ta dan jujjuya yaron a firgice Uwale tace ya haka ne? So kike ya fadi? Zulai tace a'a fa Uwale gani nayi kamar baya motsi. Kinga fa ko kuka baiyi ba. Allah tsine mai karya ta fada tare da karbe dan. Ai kuwa abinda zulai ta fada gaskiya ne. Uwale ta juya shi shiru ba motsi. Yaro ga shi fari kato ga kyau amma bai zo da rai ba. Da cangala kafar uwale ta fita kiran nurse kuzo ku daba min dannan na shiga uku na ni Hadiza ina zan sa kaina. Nurse tazo tace a'a maimunatu baki fada musu yaron bashi da rai bane? Hawaye ne ya sauko mata tace yanzu zan fada. Tani ta zauna gefen gadon ta rungumeta. Yi hakuri Munari Allah Yasa mai ceton mu ne Ya yi masa rahma. Mal Yakubu ya ajiye Sadi ya karbe yaron daga hannun Uwale ya kare masa kallo sannan ya rufe shi sosai da zanin. Uwale cikin kuka tace yanzu mai kyan ne ya mutu? To wallahi kasa a ranka Yakubu kamar kayi aure ka gama. Kan uba ni zaki yiwa haka munari? Ki haifi bakake digirgir farin kuma ya koma. Yar purse dinta ta dauka tace Zulai zo mu tafi gida. Daga bakin kofa tace tsakanin na dake munari Allah Ya isa, muguwa mai bakar aniya.
Suna fita Tani tace gaskiya baban Ramlah abinda Inna tayiwa Munari bata kyauta ba. Wannan wane irin rashin imani ne. Mace ta rasa danta a rinka binta da bakaken maganganu. Wallahi sai na fadawa Yaya Salihu ai ba daga sama ta fado ba tana da dangi. Munari tace Yaya Tani kiyi hakuri don Allah. Ya zaki bani hakuri bayan ke aka batawa Munari... mal Yakubu ya rinka bata hakuri. Yaya Salihu mutumin kirki ne amma akan yan uwansa bashi da kyau duk da kasancewar ba uwa daya suke ba amma iyayensu na zaman lafiya. Jafaru ta kira danta mai kimanin shekaru takwas. Yana shigowa yace Umma Munari sannu. Ta dan murmushi yauwa dan albarka. Tani ta goya masa Sadi ta rike hannun Ramlah. Bari mu tafi munari yaran nan basu ci abinci ba na taho dasu. Mal Yakubu ya kara bata hakuri. Yanzu zamu taho muma zan nemo dan tasi ne saboda jikinta.
Batul Mamman💖
FARAR HAIHUWA💰3
Mal Yakubu ya fito da dan kudi daga aljihunsa ya nuna mata. Kinga na ajiye saboda siyan rago amma tunda haka Allah Ya qaddara mana sai ki fada min abinda kike so na saya miki. Tasan duk don ya kwantar mata da hankali ne saboda abinda inna Uwale tayi mata. Tace haba baban Ramlah ka bari muje gida mana. Ya girgiza kai kinsan Allah maimunatu bana son Yaya Salihu yaji zancen nan. Kinga lokacin haihuwar Sadi da inna ta hana a yanka masa rago cewa yayi na sake ki ba dole bane auren. Maimunatu bazan iya rayuwa da wata mace ba bayan ki. Don girman Allah kada ki bari a raba mu. Murmushi tayi bata manta yadda ya rinka rokon yayanta ba har saida iyaye suka shiga maganar. Tace ni da kai Malam Yakubu mutu ka raba. Dariya yayi sosai sannan ya fita neman taxi da zata kai su gida.
A tsakar gida Inna uwale da zulai suka zauna tana ta bambami tun a hanya. Ni munari zata cuta? Ni uwale wallahi sai anyi min farar haihuwa a gidan nan. Sai naga jika mai kyau da daukar hankali zulai, sai jikana mace ko namiji yayi kudi. Ni banda abin namiji ma ina tsiya ina bakar fata. Munari fa banda hakora ni ban taba ganin wani abu mai haske a jikinta ba. Zulai dai sai bada baki take don tana samu a wurin aminiyar tata. Bayan sunci abinci Uwale tace ke ni a ina zaki samo min farar mace bazawara mai 'ya'ya ne.? Zulai ta ware ido farar bazawara mai 'ya'ya fa kika ce uwale. Eh saboda su hadu da dannan su haifi farare. Ko wacce iri ce indai fara ce ina so. Don ma duka yaranki sunyi aure ne ai da ko Sabuwa ya aura dama ita naso masa tuntuni. Zulai tace to zan duba Uwale gashi kinga Sabuwan ma suna ta fada da mijin gashi haihuwarta biyu. Dan karen kwadayi gare da zulai duk talaucin gidan Uwale sun fita arziki nesa ba kusa ba ga rashin abinci. Uwale tace ki barta a gidanta a samo wata saboda idan an kashe auren sai tayi idda fa. Ni kuwa so nake nan da sati biyu ma amarya ta tare. Zulai tace to bari na tafi kinsan da zafi zafi ake dukan karfe.
Gidan Sabuwa ta nufa ta tarar da ita da mijin suna fada saboda babu abinci a gidan ga yaranta suna jin yunwa. Zulai ta zakalkale kamar ba suruka ba yana ta basu hakuri suna zaginsa. Karshe zulai tace kaga Inuwa ka sakar min 'yata yanzu wallahi ko in hadaka da 'yan sanda. Yaro mara kunya haka ko yau ka saketa zata sami mijin aure. Ai farar mace kadara ce. Idan kaki kuma wallahi sharri zan kulla maka wanda zaisa ka raina kanka. Yace haba Gwaggo meyayi zafi haka? Ni bazan saketa ba. Sabuwa tace Gwaggo ban fa gaji da auren ba kawai don babu abinci sai kice ya sake ni. Ta zumburo baki. Zulai ta make bakin banza zan miki gata kina min fitsara. Zulai ta ja hannunta suka shiga daki ta fada mata hadin da take son yi. Kinga idan kika haifi farin da uwale ke jarabar so wallahi sai yadda muka yi da ita. Kina kallo dai yadda kike wahala nan ga fararen 'ya'yan shegen mijinki baya gani. Sabuwa ta bata rai Gwaggo nifa ina son sa gaskiya. zulai ta saki wata ashariya Sabuwa zan miki rashin mutumci fa. Bar ganin ni na haifeki bani da kyau a harkar samu. Ki tada balli a daren yau ya sallameki kawai.
Batul Mamman💖
FARAR HAIHUWA💰4
Sabuwa duk abin duniya ya isheta saboda yadda Zulai ta rinka yi mata fada. Tana kwance kan katifarta zuciyarta tana mata saka da warwara. Inuwa ne ya shigo dakin ya nemi kwanciya kusa da ita. Wani tsami ne ya daki hancinta ta mike cikin fada. Don wulakanci banda rashin abinci a gidanka kullum sai ka kwanta min kana wari? Don Allah ni ka tashi jiki sai tsami kamar kayi wanka da kwata. Ya tashi ya kai mata duka ta rike hannun sannan ta kwada masa wani kwantareren takalmi a ka. Cikin karaji ya biyota waje suna ta fada sai ta tuna hudubar zulai. Nan da nan ta fara zaginsa tana cewa ya saketa sanin cewa yana da saurin fushi. In sake ki ko Sabuwa? Ni kike cewa na sake ki ko? Ta eh in dai ka haifu cikin uwa da uba. Ransa ya kara baci har kin manta sakin da nayi miki kwanaki Zulai ta rinka hadani da Allah na mayar dake ko? Ai da kenan Inuwa yanzu kuwa na gaji bazan zauna yunwa ta kashe min 'ya'ya ba. Yayi dariya makota duk sun saba jinsu kije Sabuwa na sake ki saki daya amma wannan karon kada kuzo biko don wata zan nema. Kuma ki tafi ke kadai don a nan kika sami yaran ba dasu kika zo ba. Ita kalmar sakin kawai taji tasa kuka wallahi inuwa wasa nake don girman Allah ka mayar dani kafin kowa ma yaji. A zuciyarta fatan ta daya ya mayar da ita. Ina zata idan ta bar gidansa? Gwaggonta da kyar take ciyar da kanta gashi sauran yayyenta duk sunyi aure. Me ya kaita ma yarda da shawarar gwaggo. A wurin girki ta kwana washegari yayo fatali da ita da kayanta.
Cikin kuka ta karasa gida. Gwaggo Zulai na ganinta da kaya da kumburarriyar fuska ta tashi cikin sauri. Ya sake ki ko Sabuwa? Ai dadina dake jin magana. Sabuwa ta turo baki ta zauna kan tabarma yanzu Gwaggo baki damu da dukan dana sha ba sai saki ko. To ya sakeni amma wallahi idan baki yi min tanadi mai kyau ba sai na jawo miki magana a unguwar nan. Zulai ta rike baki lallai yar nan baki da kunya. To ki kwantar da hankalinki Yakubu zan tabbatar kin aura.
Tani duk ta zayyanawa iyayen su abinda Uwale tayi wa Munari. Babar su Tani Inno tace to ai inda sabo ta saba sai tayi hakuri. Shi kuma yaron Allah Ya jikan shi. Inna Ladi kishiyarta babar su Salihu tace Allah Ya shiryeki Jummai. A fada miki abinda tayiwa auta shine zaki wani tabe baki. Allah Ya jikan Malam amma da yana nan bazai lamunci wannan abin ba. Bari Yayan ku ya dawo daga birni Tani da kanshi zashi gidan. Inno tace haba Yaya don Allah kada ma ya sani. Yanzu sai kiji yana cewa a sako masa kanwarsa. Inna Ladi tace to tashi muje gidan. Inno tace ni ba zani ba Yaya rigima ce bana so. Inna Ladi ta sabi mayafi suka fita ita da Tani bayan ta ajiye yaran wurin Inno.
Batul Mamman💖
FARAR HAIHUWA💰5
A tsakar gida suka tarar da Munari tana iza wuta ga hayaki saboda yanayin damina icen duk ya jike. Inna Ladi tayi saurin zuwa wurin ta karba. Da kyar Munari ta iya durkusawa ta gaisheta. Inna Ladi tace haba mike...ina kike Uwale fito Allah Ya tona asirin ki. Yanzu yar ta haihu jiya, haihuwar ma mai ciwo tunda ba dan amma don tsabar wulakanci da kanta zata dora ruwan wanka da wannan icen haka? Uwale ta cangalo kafa daga daki ta fito. Idan kun damu da ita sai ku dora mata. Inna ladi tace tafiya muka yi jaje gidan kanin babanta garin kwari shiyasa tani bata same mu a gida ba . Dama tace jiyan ma ita ta dora ruwan. Haba Uwale rashin imanin naki har ya kai nan. Uwale tayi wani juyi ita ga mai kyau...ta tafa hannuwa yafi nan Ladi. Ki tambayeta abinda tayi min. Dan farin ne fa ya mutu sai wadan can gawayin kullum su nake gani a gidan nan. Sannan ace bazanyi fada ba. Inna Ladi tace Munari dauko gyalenki wallahi na gaji da wannan diban albarka. Idan yayanki ya dawo sai ayita ra kare. Tana gama magana Mal Yakubu ya shigo da dan guntun ragonsa kafi zuru. Jin abinda ake fada ya karasa gaban matarsa. Munari don Allah kada ki tafi. Inna Ladi ki rufa min asiri kada ku raba ni da ita. Hawaye ne taf a cikin idonsa Uwale na gani tace kwarankwatsa ka bari hawayen nan suka fito gaban surukarka sai na daga maka nono. Da kaji anyi zancen saki sai kuka kamar ka auri hurul...hurul me ma? .oho matan aljannah dai nake. To ka zabi daya ko ka sake tan ko kuma nan da sati biyu ka auri duk wadda na zaba maka. Da hanzari yace zanyi auren inna. Ya koma kallon Munari koma daki in dafa miki ruwan kinji. Kinga rago can na siyo zan gasa miki. Sosai Inna Ladi taji tausayinsa amma sai ta dake ni dai tafiya zanyi da ita mun gaji. Uwale tayi tsaki aikin banza kin saki baki kishiyar uwa zata kashe miki aure kin zata sonki take. Makirci ne kawai irin namu na mata. Munari sai a lokacin tayi magana.. Inna ki dena fadin abinda kika ga dama kan Innarmu don akanta wallahi zan....zaki me??? Kaji ko dan nan matarka zata zageni. Inna Ladi tace Tani dora ruwan wankan ko sake kallon Uwale bata yi ba taja hannun Munari suka koma daki.
Bayan kwana hudu da haihuwar munari Uwale na zaune karkashin bishiya tana shan fura Zulai ta shigo. Tana ganin furar yawunta ya tsinke. Ita kuwa uwale bata san tana yi ba kuma bata yi mata tayi ba. Can ta lura da kallon da Ramlah ke yi mata. Ta ja tsaki shegiya mayya duk ta kafa min ido zo ki karba. Yarinya ta taso daga wurin wasanta tazo gaban uwale. Dan yatsa ta tsoma cikin furar ta dangwala mata a harshe. Ramlah ta lashe tas ta koma wasa. Zulai dai abin duniya ya isheta sai ta fara tunanin abubuwan tausayi da suka sameta kamar rashin abinci da rashin tayin fura daga kawarta. Nan da nan sai ga hawaye Uwale ta tande baki tace lafiya zulai. Uhmm ina fa lafiya Uwale. Ina ta faman nema miki yarinyar da Yakubu zai aura jiya da daddare sai ga Sabuwa. Uwale tace fara gaya min zancen yarinyar kafin muyi zancen sabuwan. Zulai ta sha kunu Uwale baki da kara fa. Aurenta fa ya mutu. Ajiye ludayin tayi eyye kika ce me? Nace aurenta ya mutu. Ashe wata biyar kenan da mijin ua saketa bata fada ba ta zauna gidan tana son ya mayar da ita gashi har iddah ta kare. Jiya yayi mata korar kare. Sai wasu hawayen ke zubuwa daga idon Zulai ganin kudaje na bin kokon furar tasan sarai uwale na gani zata zubar da ita gaba daya. Uwale tace to ai ki bar binciken haka tunda har ta gama iddah kuma na tuna duk yaranta farare ne. Ki bar komai a hannuna ranar asabar zata tare a gidan wannan alqawari ne. Zulai sai murna , uwale tace ga fura ki sha. Kafin ta rufe baki Zulai ta janye kokon ta kafa kai. Mayunwaciya Uwale ta fada a sarari.
Tana zuwa gida ta sanar da Sabuwa yadda suka yi. Ni dai na fada musu kin gama iddah idan ba haka nayi ba kinsan uwale da rashin hakuri kamar zawo sai ta bashi wata. Sabuwa ta hadiyi yawo da kyar tace Gwaggo ina jin ciki gareni fa wata kusan biyu. Muhuci zulai ta kwala mata a ka. Baki da aiki sai ciki ne duk yunwar gidan inuwa. To bari kiji. Ranar asabar zaa daura aurenku sai kiyi shiru da bakinki. Idan kika haihu sai muce bakwaini ne.
Batul Mamman💖
FARAR HAIHUWA💰6
Sabuwa ta ware idanu kai Gwaggo ai kinga auren babu iddah ma ba kyau ko? Zulai ta banza rufe min baki. Inji uban wa aka ce ba kyau. Aure kan aure ne ba kyau kuma dai ba shi zakiyi ba tunda ya sake ki. To cikin fa? Shi ciki ai ba matsala kinsan Uwale babu abinda ba zatayi ba akan farin jika. To nasan tana da gonaki biyu na gadonta kinga ko ita muka samu mun huta. Sabuwa dai bata gamsu ba tace Gwaggo zunubin fa. Ai dan zai zama shege...kul kika kira shi shege da ubansa fa. Ina fata bai san da cikin ba? Eh bai sani ba. Zunubin kuma zamuyi ta cewa astangafirillah sai kiga Allah Ya yafe. Sabuwa tace Astagfirullah dai Gwaggo. To naji yanzu dai kin amince ko. Na amince Gwaggo. Sukq zauna suka kulla duk yadda zasuyi a gidan Uwale idan aure ya yiwu. Saar su daya kauyen da Sabuwa ke aure daban da nasu saboda haka da wuya yaji labarin auren.
Shirye shirye ya kankama na bikin Sabuwa da Mal Yakubu. Uwale da Zulai le kidansu da rawarsu don shi angon ko a ransa. Kullum yana rarrashin Munari ta kara hakuri idan ya sami kudi zai raba musu gida da Inna Uwale. Ana saura kwana biyu Yaya Salihu yazo garin Danmarka gaida iyayensa shi da matarsa Ruma. Tani na jin labarinsa ta tafi gidan ta zayyana masa halin da Munari ke ciki. Fada ya rinka yi iyakar karfinsa Inno tana bashi hakuri. Inna Ladi tace ni bazaka burge ni ba sai kaje gidan kayiwa uwarsa barazana yadda zata yi shayin takurawa 'yata. Kamar jira yake ya tafi gidan cikin fushi. A bakin kofa ya gamu da Mal Yakubu ya fara zazzaga masifa. Mal Yakubu duk ya tsorata yana ta bashi hakuri. Har gidan ya shiga sukayi ta da Uwale yace ke Maimuna dauko mayafinki ya kama hannun yaran..birni zamu tafi kai kuma ka biyoni da takardarta. Mal Yakubu dai harda kuka itama Munari tana yi. Da kyar Yaya Salihu ya aminci ya barta amma ya dauke Sadi dashi zan tafi. Mal Yakubu yace wallahi na bar maka shi don girman Allah kada ka rabani da matata. Yaya Salihu yace mata zan kaiwa Ruma kinji ko munari sai ta hada shi da Ali su shiga makaranta idan sun dan kara girma. Godiya tayi masa ya kawo kudi ya bata. A waje ya sake jaddadawa Mal Yakubu ya kular masa da kanwa sannan idan anyi auren zai sa ido a kansa. Daidai da rana daya yaji zance mara dadi zai dauki mataki.
Ranar lahadi da karfe biyun rana bayan an idar da sallar azahar aka daura auren Mal Yakubu da Sabuwa. Dakinsa aka saka amarya ya zama bashi da daki a gidan sai na wadda take da girki. Da daurin gindin uwale Sabuwa ta goge da yiwa Munari wulakanci a gidan. Kullum hakuri take saboda yadda mijinta ke iyakar kokarinsa wurin kyautata mata. Watan Sabuwa biyu a gidan ta fara bayyana cikinta kamar yadda suka yi da Zulai. Uwale kamar ta lashe ta don so. Kullum Zulai tana gidan abinci safe ,rana da dare duk an mata kwano. Habaici iri iri Munari take sha idan suka hade kansu karkashin bishiya da yamma. Kirikiri Uwale ta hana Sabuwa girki kullum Munari keyi idan dare yayi kuma ta tubure tace sai Mal Yakubu ya shigo dakinta ranar girkinta.
Batul Mamman💖
FARAR HAIHUWA💰7
Haka rayuwa ta kasance a gidan Mal Yakubu yau fari gobe tsumma a wajen Munari. Ba don soyayyar da suke ma juna ita da mijinta ba da tuni ta bar gidan.
Sabuwa na kwance a kofar dakinta da daurin kirji tana shan rake Uwale ta fito daga bandaki tace kai sabuwa ki raba kanki da zaki fa saboda nakuda. Kinji ki Inna kamar wata sabon shiga? Haihuwa ta uku har sai kin karanta min yadda zanyi? Ta yatsina fuska ke fa daya kawai kika yi ta tsaya miki cak. Munari daga cikin dakinta tace Allah Ya kara ta cigaba da yiwa yarta Ramlah kitso. Uwale har wani tsoron sabuwa take ta ajiye butar hannunta tace to Allah Ya baki hakuri uwar biyu. Wannan ciki naki badai girma ba. Gaban Sabuwa ya fadi ita bata taba ciki mai girman wannan ba ma gashi a karyar da tayi baifi wata bakwai ba. Bata sake tankawa Uwale ba don kada a ja maganar ta cigaba da shan rakenta.
Bayan sati uku wata rana Uwale da zulai sun fita unguwa tun safe nakuda ta kama Sabuwa. A muguntar Uwale kulle gidan tayi ta waje wai kada munari ta fita saboda taji Mal Yakubu yana cewa ta dawo da wuri tasan sarai unguwa zata. Da munari ta shirya ta shirya yarta zasu fita taji kofar a garkame. Ta gaji da ja ta dawo daki rai a bace. Dama gidan kanwar Inno zata je ziyara. Tana ajiye gyalenta taji kamar ana kiranta daga dakin Sabuwa. Shiru tayi ta tabbatar sannan ta fito cikin sauri. A kwance ta ga Sabuwa tana nishi da kyar duk ta hada gumi duk da sanyin gari. Munari jika na rawa don itama bata saba ba tace Sabuwa kinga Inna ta kullemu ta waje kuma saboda zurfin soro babu mai jinmu kiyi hakuri na dubaki. Cikin masifa tace kiji dadin kasheni ko...ki fita ki nemo taimako Munari don idan na mutu sai nayi miki fatalwa. Babu irin bugun da Munari batayi ba babu wanda yazo kashe reza ta samo a daki ta dawo kan sabuwa. Tace kiyi hakuri inajin bakwaini zaki haifa don kai ya fito. Da taimakon Allah Munari tana ta yi mata addua ta samu Sabuwa ta haihu. Yarinya ce santaleliya fara tas irin wadda Uwale take so. Munari ta yanke cibi ta taimaka mahaifa ta fito. Kai Sabuwa wannan 'ya da takai wata tara ban san irin girman da zata yi ba. Ruwan wanka ta dora ta wanke jaririya ta kaiwa sabuwa ruwan wanka. Sai bayan laasar Uwale da zulai suka dawo. Tun daga tsakar gida uwale ke yiwa Munari dariyar keta ta hanata fita. Munari ko a jikinta tace Inna kinyi kawa fa. Ko kulata bata yi ba harda tsaki zata wuce tace Inna nace kinyi kawa fa Sabuwa ta haihu. Zulai ta yi dakin cikin sauri Uwale tana binta tana cangala kafa. Allah Kasa fara ce, Allah Kasa fara ce. Haka take fada har ta shiga dakin. Baby ta dauka ta rungume. Yarinyar akwai kyau ga hasken da Uwale ke buri. Zulai ta rike yarta. Sabuwa bakwaini kika haifa? Me ya faru haka? Waya karbi haihuwar? Sabuwa tace nakuda ce ta kamani gashi kun kulle gidan. Munari ce tayi komai, Uwale ta rungume yar ta fita. Munari ta gani tana kwasar tuwo ta dan saki fuska nagode fa Munari sannu da kokari. Zulai da ta gama zige yarta a cikin daki ta fito da sauri wace godiya zakiyi mata uwale? Ashe kina fita ta kama Sabuwa da kokawa shine haihuwar tazo ba shiri. Ai don kada a kamata da laifin kisa ta karbi haihuwar. Uwale ta bata rai muguwa azzaluma da mai kyan zaki kashe min. To ta Allah ba taki ba baka mai bakar aniya. Tuwon ma bazata ci ba kada kisa guba. Kwashe abinki ki bace min da gani. Hawaye ne ya saukowa Munari ta je har kofar dakin ta leka Sabuwa na kwance a kan gado. Cike da takaici tace Sabuwa abinda zaki saka min dashi kenan ko? Allah na gani kuma baya bacci. Zulai tayi tsaki muguwa kinga farar haihuwa kina bakin ciki.
Mal Yakubu dai yayi farinciki daidai gwargwado yace to Inna sai asa mata sunanki ko. Tunda kan Ramlah kika ce kada asa sunanki. Uwale tace yo haka kurum zaka sawa wancan mummunar abar sunana? Ya jawo abarsa ya rungume suk yaransa yafi sonta. Inna tace itama wannan bazaka sa mata sunana ba saboda kyanta. Akwai sunan gayu dana taba ji wallahi wata rana dana je gidan Harira jikanta ya kunna talabijin. Sabuwa tace ni fa Inna kada ki bata wa yata suna. Inna tace ni dai Hannan naji an fada ai ko yayi dadi ko? Sabuwa ta bata fuska Hannan kamar marowaciya Hanan ake cewa. Na yarda Malam a saka mata. Mal Yakubu yace to Allah Ya raya ya dauki Ramlah ya tashi yayi waje.
Ranar suna aka radawa yarinya suna Hanan. Uwale sa guda ta bayar aka yanka cikin shanunta uku. Anyi bushasha ranar suna kamar haihuwar fari. Yan uwan Sabuwa suna ta zuba habaici ga Munari. Ga 'ya mai goshin arziki an haifa. Haka dai akayi ta taro Munari da nata yan uwan suna daga cikin daki. Yayar sabuwa na suyar nama ta bawa duka yaransu aka tsallake Ramlah. Ta rinka binsu da kallo har Uwale ta kula tayi tsaki ai idan baki bata ba Hanne yarinyar nan kamar mayya sai tasa ki kone da mai. Cillo mata kashi ta gwaigwaya. Hanne ta dauko wani guntun qashi ta jefawa Ramlah. Qashin bai zame ko ina ba sai bakin rijiya Ramlah ta bishi da dan gudunta. Tana zuwa bakin rijiyar takalminta daya ya zame daga kafarta santsi ya kwasheta sai cikin rijiya.
FARAR HAIHUWA💰9
Sai da cikin Munari yayi wata shida Uwale da sabuwa suka san dashi. Gaba daya Sabuwa hankalinta a tashe yake tana tsoron kada Munari ta sake haihuwa hankalin Mal Yakubu ya koma kan abinda ta haifa. Yanzu ma kamar yasan Hanan ba yarsa bace baya bi ta kan ta sai Inna Uwale ta dame shi. Ita kuwa kullum tana rike da ita a tsakar gida ko dakinta tana mata waka. Hannan farar jikar Uwale. Zaki auri mai kudi mai mota,zaki kaini makka da madina.
Duk wahalar da Munari ke sha saboda cikinta yakai watan haihuwa Uwale bata daga mata kafa akan girki ba irin yadda aka yiwa Sabuwa gata. Ganin aka Mal Yakubu ya siyo risho har biyu yasa a kitchen din. Uwale bata san dashi ba sai da ta fito da goyon Hanan tana ta cangala yar kafarta. Eyye me zan gani haka? Fito fiti kinibabbe ta kirawo Mal Yakubu daga daki. Wato don munafurci shine zaka wani siyo risho saboda matarka ta dena wahala ko? To ban yarda ba. Ni nafi son abincin da aka dafa da itace. Yafi dadi da inganci. Sabuwa tace a'a fa inna waye baya son sauki ni gaskiya nafi son rishon. To...to ai shikenan saboda kada fatarki tayi duhu a bakin murhu ba. Ta harari Munari kunyi sa'a uwar mai kyau tana son rishon ba don haka ba da kunga tsiya wallahi. Kamar kullum shi dai Mal Yakubu sai aikin bada hakuri.
Tun dare Munari ke fama da ciwon baya kadan kadan tana daurewa. Zuwa asuba abin ya ta'azzara gashi ba girkinta bane. Da kyar ta iya mikewa ta bude kofar dakinta. Dakin Inna uwale ta nufa tana tafiya da kyar. Tana ta kwankwasawa Uwale na jin muryarta ta sake gyara kwanciya....aikin banza haihuwa ta hudu ai zaki iya da kanki. Haka ta koma kofar dakin Sabuwa tana bugu. Mal Yakubu ne ya fito ya kamata zuwa dakinta yace Sabuwa ta tashi Inna su kula da ita sannan ya fita zuwa gidan makocinsa mai akori kura ya taimaka masa su tafi asibiti. Yana dawowa daga bakin kofa ya jiyo kukan jariri. Da gudu ya karasa ya ganta kwance kan tabarma ita kadai da baby a gabanta. Duk ya rude yace bari na kira Inna...hannu ta daga masa barshi kawai Malam ga reza can dauko ka yanke cibiyar.
Su kadai suka yi abinsu su Inna ko leqe. Ya fita ya bawa makocinsa hakuri ya dawo ya buga kofar daki cikin fushi. sabuwa ki fito kafin na shigo dakin nan don wallahi na shigo jikinki zaiyi tsami. Ta fito tana mika...yanzu don wulakanci ince ki tashi inna ku taimakawa Maimunatu sai ku barta ita kadai? Inna ta fito dan nan ni kake cewa munyi maka wulakanci? To mungode Baba sai ka fadi me kake so muyi yanzu. Inna ni ba haka nake nufi ba amma ai ko sannu ayi mata. Sannu maigida to me aka samu? Mace ce ya fada ya kasa boye murnarsa.
FARAR HAIHUWA💰8
Salati da ihun mata yasa su Munari fitowa daga daki. Mata na ganinta suka yi cirko cirko an rasa mai magana tana ta tambayar me ya faru. Uwale tace ni dai ba ruwana ,fa bani bace. Munari tace wai meye ne? Me kuke leqe a rijiyar? Wata makociyarsu ce tayi karfin halin fada mata...Ramlah ce ta fada.
Wata kururuwa Munari tayi cikin zafin nama ta nufi rijiyar ana rirriketa. Tani tace cikin rudewa garin yaya ta fada? Wata yar cin shinkafar sunan tace qashi ne Hanne ta jefa mata bakin rijiya shine ta bishi ta fada. Mal Yakubu aka fita kira a majalisarsu. Munari tun tana kuka da sauti har muryarta ta dashe....wayyo Allah kawai take cewa. Abin tausayi ta zama.
Mal Yakubu ya shigo yana tambayar me ya faru ake nemansa. Munari ta mike ta rije wuyan rigarsa. Baban Ramlah idan na rasa 'yata bazan zauna a gidan nan ba. Yi hakuri ki fada min abinda ya faru. Wani yaro yana cin nama yace 'yarta ce ta fada rijiya. Mal Yakubu yace Ramlah? Babbar riga ya tube zai shiga shima aka rike shi. Uwale ta soma kuka don Allah dan nan kada ka shiga kaima ka mutu. Suna haka Sabi mai hakar rijiya ya shigo da wasu maza. Igiya mai kauri aka daura masa ya shiga. Duk sakan a wurin su Munari tamkar shekara suke jinsa. Kamar wata zautacciya haka ta koma. Sai bayan kusan minyi goma ya fara jan igiyar. Cikin sauri aka jawo shi da Ramlah a kafadarsa. Mal Yakubu ya karbe ta ya kwantar akan tabarka. Cikinta ya danna ruwa y rinka fita ta bakinta da hanci. Munari ko wurin bata je ba tana zaune inda wasu mata suka riketa ta share hawaye Allah Ya jikanki Ramlah kawai take fada.
Duk yayi iya yinsa ya tabbatar yarsa ta rasu. Cikin kuka ya bude hannun da yaga ta damke sosai. Qashin data dauka ne ashe ba rabonta bane. Wace 'yar....din ce ta jefa kashin bakin rijiya? Jin kowa yayi tsit ya sake kunduma zagi cikin tsawa. Aka samu wata ta nuna Hanne. Kanta yayi kamar zaki cikin fushi wani abokinsa ya rike shi. A tsorace tace Uwale ce tace min mayya ce na jefa mata qashi shine tautsayi yasa na jefa bakin rijiya. Suna wannan fadan Munari ta dauke gawar yarta ta kai daki ta fara shirin yi mata sutura. Taron suna ya koma na mutuwa ita dai Uwale tayi tsit don yau dan nata ya bata tsoro. Yana matukar son Ramlah sosai. Bayan an tafi kaita ne Munari tana zaune gaban iyayenta da suka zo ta fara jan numfashi da kyar. Mal Yakubu aka kira ya zo ya fitar da ita a rude. Ya kalli innarsa cikin bacin rai. Idan itama ta mutu yau zan saki Sabuwa kuma ta tafi da yarta bana so. Asibiti suka nufa inda likita ya tabbatar jininta yayi mugun hawa kuma tana dauke da ciki na wata daya. Duk da bakin cikin dake damunsa Mal Yakubu yayi matukar murna. Ta taga yake leken matarsa saboda ance a barta ta huta sosai. Yana adduar ta sami lafiya.
Bayan kwana takwas da rasuwar Ramlah Inna Ladi tazo gidan da sauran yaransu mata hada kayan Munari. Mal Yakubu yana ta bada hakuri yana zubar da hawaye. Inna Ladi tace kaga ka bari mu tafi ta laluma kafin yayanta ya zo kaima tunda baka ganshi ba kasan baya gari ne. Kiyi hakuri inna ya zan saki Maimuna a wannan lokacin ga rashin 'ya ga kuma rabo a tare da ita. Inna Ladi ta kalle ta Munari da gaske ne? Kanta ta sunkuyar kasa sai hawaye. Yi shiru kinji kada ciwonki ya tashi. Ta dubi Uwale dake zaune tana yiwa Hannan rawa Sabuwa tana bacci a daki. Yakubu kasan kashe min jika akayi da gangan muka hakura yanzu haka zata zauna cikin bakin cikin rayuwa a gidanka? Kiyi hakuri inna babu fa wani yanayi mai dorewa. Zan kula da ita muddin raina bazan bari wani ya wulakanta ta ba,yana magana yana kallon Inna Uwale. Ta dago kai nasan dani kake dan nan ka cigaba da zargina don kawai yarka ta mutu. Ba ga wata Allah Ya baka ba? Girgiza kai yayi ya cigaba da bawa su Inna hakuri.
Tun daga lokacin babu me shiga harkar Munari a gidan saboda yadda iyayenta suka sa musu ido. Sai habaici daga gefe. Mijinta kuma yana nuna mata so da kulawa sosai suna ta rainon cikinta cikin sirri. Wata rana suna cin abinci tace ni kuwa Mal meyasa baka so su inna su san ina da ciki? Munari kenan ai ba murna zasu yi ba. Karshenta a rinka yin abinda zaa bata miki rai har ciwonki ya tashi. Ko kin manta Yaya Salihu yace duk ranar da jininki ya hau ko zanyi kukan jini sai na sakeki. Dariya tayi masa aikuwa gobe zanyi masa aike. Au tsokanata ma kike ko? Zan rama ne... yanzu dai kiyi ta sa hijab da zaman daki so nake kawai Inna taji haihuwa. Allah ba don darajar ta haifeni ba da tuni nasa an daure....hannu tasa ta rufe masa baki. Haba Mal? Ka manta Allah Yace kada mu fadi kalma mara dadi game da iyayenmu? Kada ka manta kwananta ne ya kare mu kuma hakurinmu shine ladanmu. Hakane Munari nima yau na dana. Allah Yayi miki albarka Ya saukeki lafiya. Amin Malam
FARAR HAIHUWA💰10
Inna uwale ta tabe baki sai mace ta takarkare ta haihu amma karshe kaga bakin jariri. Allah Ya raya dauko min abin na gani a nan bana son doguwar tafiya saboda kafa. Ba musu ya je ya dauko mata 'yar da kansa ya kawota. Ba yabo ba fallasa itama dai bakar ce amma ba sosai ba gata kyakkyawa kamarsu daya da mal Yakubu. Inna tana kallonta ta mika masa gata nan bari naje nayi sallah. Ita kuwa Sabuwa ko kallon yar bata yi ba ta juya zata koma daki. Dawo nan ya daka mata tsawa. Wuce kije ki dora mata ruwan wanka. Inna uwale tace ka ma isa...ita da take da jaririya. Dama ai gasa ce tasa munarin haihuwa yanzu. Girgiza kai yayi cike da takaici yaje ya dora ruwan da kansa.
Daga ranar 'yan uwan munari ke yi mata komai. Ana saura kwana biyu suna tace Mal wane suna zaka saka mata ne? Haba munari ai shawara zamuyi dake. Ta sunkuyar da kanta kasa nasan wanda ya mutu baya dawowa amma inda hali a saka mata Ramlah. Murmushinsa ya fadada dama haka naso ina dai tsoron yi miki fami ne. Allah Ya raya mana ita. Tace amin. Uwale dake bakin kofar dakin ita da Zulai wanda dama gulma suka zo ji ta shigo tana matsar kwalla. Yanzu dan nan ko kara bazaka min ba kasa sunana sai zabin matarka. Inna ke fa kika ce ba kya so tun a haihuwar marigayiya. Akan Hanan ma kika sake cewa bakya so kika zaba mata wanan sunan. Ta dan fito da ido ni dan nan? Abin harda sharri? To ba damuwa ka saka mata sunan da kake so. Tana juyawa zata fita Munari tace haba Inna kiyi hakuri sunanki za'a saka mata. Ba haka inna uwale taso ba, so tayi Munari ta ce bata son sunan sai ta hadasu fada da Yakubu. Tsaki tayi ta fice Zulai na rufa mata baya. Duk da abin baiyiwa munari dadi ba sai ta nuna wa Mal Yakubu jindadinta sosai.
Ranar suna aka radawa yarinya suna Khadija. wata yar uwar baban Mal yakubu ce tazo ta karbi jaririyar wanzami yazo za'a cire mata beli. Uwale ta gama lura da yadda munari ke matukar kaunar jaririyarta sai ta fita wurin wanzamin tare da waziriyarta zulai. Basu dade da fita ba aka jiyo sautin kukan Khadija da katuwar murya kamar zata shide. Mata an sami abinyi suka yo soro da gudu. Tani ce kan gaba tana zuwa ta tarar uwale ta kwaye gefen fuskarta wanzan yana kallon kalangunta ya fara zanawa jaririya a gefen fuskarta na dama. Fizgota Tani tayi ta koma cikin gidan da sauri. Munari ta karbeta zata bata nono amma taki karba sai wani irin kuka take. Har dakin Uwale ta biyosu. Amma Tani baki da ta ido. Yanzu nace ayiwa yarinya kalangu zanen fulani irin nawa shine zaki dauketa. Munari tana hawaye tace yanzu Inna duk gidan nan wa aka taba yiwa zane a fuska shine zaki ce ayi mata. Au kema rashin kunyar zaki min? Bani ita a karasa mun barshi a zaune. Munari tasa zani ta goya yarta tana ta kuka. Wallahi Inna idan kinga anyi wa yarinyar nan zane a fuskarta to mutuwa nayi. Ya kike so nayi da raina ne? Matsalar yau daban ta gobe daban. Allah bari Mal ya dawo idan mutuwar aurena ce tazo sai dai na tafi da yata. Zanen nan fa Allah Ya tsinewa maiyi da wanda akeyiwa. Kuka wiwi Uwale tasa ita a dole anyi mata rashin kunya. Nufinki Allah Ya tsine min ko? To yau zanga wanda dan nan zai zaba cikin mu biyu.
Daga gefe wasu mata suka ce gidan uwale duk taron suna sai anyi dirama. Ai munari ta kyautawa kanta yau.
FARAR HAIHUWA💰11
Wasa wasa har magariba ta gabato ana ta mayar da zance a gidan Mal Yakubu. Shi dai tun a kofar gida da labari ya riske shi komawa yayi ya kira wan babansa Baba Hadi.
A tsakar gidan ya tarar dasu gaba daya da sauran mata 'yan jin kwakwaf. Baba Hadi na shigowa yace duk su fice su bar gidan. Sum sum suka rinka fita daya bayan daya. Ba dai haka aka so ba don sun so jin yadda zata kaya aji dadin ba da labari. Suna fita Inna Uwale cikin kuka take labarta masa abinda ya faru. Baba Hadi yace ba matsala ke Munari bani yar . Ba musu ta mika masa jaririyar bayanta. Yace to Yakubu karbo yayarta ya nuna Hanan dake hannun Sabuwa. Bari na sa Yau ya kira wanzamin duk sai ayi musu. Shima Sadi idan suka zo gari sai a karbo shi a yi masa. Uwale ta wurgo kafa cikin sauri bangane ba Yaya Hadi wai harda Hannan za'ayi wa? Eh ya amsa a takaice. Dukkansu ba jikokinki bane? Tayi tsuru tsuru da ido...anya ayi harda ita? Sabuwa ta ce Al-Quran ba za ayi mata ba. Mal bani 'yata. Baba hadi yace au ita wannan da baki isa da uwarta ba shine zaki ce kada ayi mata, amma ita munari ko kadan baki damu da lamarinta ba? To wallahi ki fita idona Uwale. Akan yadda kike takurawa matar yaron nan zan nuna miki ni ba marigayi bane. Shine yake jure halinki na tsiya. Kai ta sunkuyar kasa bata ce uffan ba. Ya mikawa munari yarta. Ki kara hakuri kinji Maimunatu. Allah Ya raya muku yaranku. Tana ta godiya ya fita Mal ya raka shi.
Tun daga lokacin uwale ta kara kunnawa Munari karan tsana. Duk lokacin da Mal Yakubu ya fita sai wulakanci kala kala. A can birni kuwa Yaya Salihu yasa Sadi a makaranta tare da yaransa. Lokacin da Ummita ta shiga wata na ashirin da haihuwa Munari tayi shirin yayeta. Wata rana tana kwasar tuwo Ummita tana ta zillo a bayanta. Tace haba mamana so kike na kona hannu ne? Uwale wadda tuni zulai ta bata shawarar yadda zata kori munari daga gidanta ta daga waje ni kuwa munari kin fiye kinibibi yaushe ta zama mamanki. Na zata sunan uwarki Baraatu. Munari tayi murmushi Inna ai kema uwata ce. To indai haka ne daga yau tunda dai nike da iko da kowa a gidan nan yarinyar nan zaa rinka kiranta Dijengala. Ni na tsani suna Ummita dinnan. Gara dai a kirata dijengala a gargajiyance. Munari tace to ba komai inna ai yadda kike so haka zaayi. Ba haka inna uwale taso ji don fada tazo takala. Sabuwa ta fito daga dakinta tace inna kinji da yadda ta amsa miki kuwa? Ai gatse tayi miki. Allah Ya kyauta uwar miji ace bata isa da surukarta ba. Ni kina ji ai sanda ta sawa tawa yar suna. Wannan ma idan na haife ita zata sa suna.
Munari dai bata kula ba don tasan neman rigimar tasu ne ya tashi. Da Uwale taga haka zama tayi a wurin sai da mal yakubu taji sallamarsa tasa kuka. Karya da gaskiya ta rinka hada masa Sabuwa na mara mata baya. Ganin ko kadan bai yarda ba tace kai na gaji so nake indai ba tare na haife ku ba ka saketa ta koma gidan ubanta. Munari ta soma hawaye tana bata hakuri. Ta tabe baki kyayi kya gama. Yau abincinki ya kare a gidan nan. Idan baka saketa ba yanzu a gabana ba wallahi sai na tsine maka albarka. Haba inna ya kike so nayi ne? Babu abinda kike nema da bana miki. Don Allah kiyi hakuri. Itama kukan tasa masa idan baka saketa ba Allah Yakubu zan maka mugun baki. Naki jinin bakar matar nan. Ka saketa yanzu.
Munari tace mal idan kana son gamawa da duniya lafiya kabi umarnin Inna. Yana kuka tanayi yace na sakeki saki daya. Wani kukan ne ya zo mata da karfi ta shiga daki dauko mayafi. Inna don ta kara kuntata mata tace kwanto goyon ai ba dashi kika zo ba. Dama yar ta isa yaye. Munari ta kalli mal yakubu yace Inna don Allah. .hannu ta daga Allah Ya tsi....da sauri munari ta kwanto yar da take matukar so ta bashi ta fita daga gidan cikin kuka.
FARAR HAIHUWA💰11
Wasa wasa har magariba ta gabato ana ta mayar da zance a gidan Mal Yakubu. Shi dai tun a kofar gida da labari ya riske shi komawa yayi ya kira wan babansa Baba Hadi.
A tsakar gidan ya tarar dasu gaba daya da sauran mata 'yan jin kwakwaf. Baba Hadi na shigowa yace duk su fice su bar gidan. Sum sum suka rinka fita daya bayan daya. Ba dai haka aka so ba don sun so jin yadda zata kaya aji dadin ba da labari. Suna fita Inna Uwale cikin kuka take labarta masa abinda ya faru. Baba Hadi yace ba matsala ke Munari bani yar . Ba musu ta mika masa jaririyar bayanta. Yace to Yakubu karbo yayarta ya nuna Hanan dake hannun Sabuwa. Bari na sa Yau ya kira wanzamin duk sai ayi musu. Shima Sadi idan suka zo gari sai a karbo shi a yi masa. Uwale ta wurgo kafa cikin sauri bangane ba Yaya Hadi wai harda Hannan za'ayi wa? Eh ya amsa a takaice. Dukkansu ba jikokinki bane? Tayi tsuru tsuru da ido...anya ayi harda ita? Sabuwa ta ce Al-Quran ba za ayi mata ba. Mal bani 'yata. Baba hadi yace au ita wannan da baki isa da uwarta ba shine zaki ce kada ayi mata, amma ita munari ko kadan baki damu da lamarinta ba? To wallahi ki fita idona Uwale. Akan yadda kike takurawa matar yaron nan zan nuna miki ni ba marigayi bane. Shine yake jure halinki na tsiya. Kai ta sunkuyar kasa bata ce uffan ba. Ya mikawa munari yarta. Ki kara hakuri kinji Maimunatu. Allah Ya raya muku yaranku. Tana ta godiya ya fita Mal ya raka shi.
Tun daga lokacin uwale ta kara kunnawa Munari karan tsana. Duk lokacin da Mal Yakubu ya fita sai wulakanci kala kala. A can birni kuwa Yaya Salihu yasa Sadi a makaranta tare da yaransa. Lokacin da Ummita ta shiga wata na ashirin da haihuwa Munari tayi shirin yayeta. Wata rana tana kwasar tuwo Ummita tana ta zillo a bayanta. Tace haba mamana so kike na kona hannu ne? Uwale wadda tuni zulai ta bata shawarar yadda zata kori munari daga gidanta ta daga waje ni kuwa munari kin fiye kinibibi yaushe ta zama mamanki. Na zata sunan uwarki Baraatu. Munari tayi murmushi Inna ai kema uwata ce. To indai haka ne daga yau tunda dai nike da iko da kowa a gidan nan yarinyar nan zaa rinka kiranta Dijengala. Ni na tsani suna Ummita dinnan. Gara dai a kirata dijengala a gargajiyance. Munari tace to ba komai inna ai yadda kike so haka zaayi. Ba haka inna uwale taso ji don fada tazo takala. Sabuwa ta fito daga dakinta tace inna kinji da yadda ta amsa miki kuwa? Ai gatse tayi miki. Allah Ya kyauta uwar miji ace bata isa da surukarta ba. Ni kina ji ai sanda ta sawa tawa yar suna. Wannan ma idan na haife ita zata sa suna.
Munari dai bata kula ba don tasan neman rigimar tasu ne ya tashi. Da Uwale taga haka zama tayi a wurin sai da mal yakubu taji sallamarsa tasa kuka. Karya da gaskiya ta rinka hada masa Sabuwa na mara mata baya. Ganin ko kadan bai yarda ba tace kai na gaji so nake indai ba tare na haife ku ba ka saketa ta koma gidan ubanta. Munari ta soma hawaye tana bata hakuri. Ta tabe baki kyayi kya gama. Yau abincinki ya kare a gidan nan. Idan baka saketa ba yanzu a gabana ba wallahi sai na tsine maka albarka. Haba inna ya kike so nayi ne? Babu abinda kike nema da bana miki. Don Allah kiyi hakuri. Itama kukan tasa masa idan baka saketa ba Allah Yakubu zan maka mugun baki. Naki jinin bakar matar nan. Ka saketa yanzu.
Munari tace mal idan kana son gamawa da duniya lafiya kabi umarnin Inna. Yana kuka tanayi yace na sakeki saki daya. Wani kukan ne ya zo mata da karfi ta shiga daki dauko mayafi. Inna don ta kara kuntata mata tace kwanto goyon ai ba dashi kika zo ba. Dama yar ta isa yaye. Munari ta kalli mal yakubu yace Inna don Allah. .hannu ta daga Allah Ya tsi....da sauri munari ta kwanto yar da take matukar so ta bashi ta fita daga gidan cikin kuka.
FARAR HAIHUWA💰12
Cikin kuka ta shiga gidansu da sallama. Inna Ladi ta ajiye butar hannunta ta taro ta. Me ya faru Munari? Ta shafa bayanta taji ba goyo. Ina 'yar? Ba dai ta mutu ba. Munari ta kasa magana sai kuka. Inno tace wai ba magana ake miki ba. Inna ya sakeni, inna uwale tace idan bai sakeni ba zata tsine masa. Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Ita kuwa Uwale tana son gamawa da duniya lafiya? Ina ruwanta da zaman ku inji Inna Ladi. Inno dama bata saka baki a lamarin gidan yarta saboda kara amma yau bakinciki ya isheta. An sako mata 'ya da magaribar fari. Tace ina goyon. Munari ta sake fashewa da kuka tace ba dashi nazo ba. Inno tace Alhandulillahi in anyi duniya don Manzon Allah SAW kin bar gidan Yakubu har abada. Saurin dago kai tayi haba Inno wallahi ba da son ranshi bane. Na dai fada miki...munari ba fa sadakarki aka bani ba. Haihuwarki nayi kamar kowanne da. Kyautace Allah Ya bani to nayi hakurin da zanyi Allah Ya yanke miki wahala. Inna Ladi tace hakane amma kada muyi saurin yanke hukunci.
Sallama suka ji daga waje. Inna Ladi ta amsa don ta gane mai muryar tare da yi masa izinin shigowa. Yana shiga gidan ya zube a kasa yana basu hakuri. Inno tace ai ni so nake ka cike mata sakin gabadaya. Inno kiyi hakuri don girman Allah. Zan kama mata gida sai na mayar da ita can. Kaga tun ina ganin mutumci da kimarka ka bar gidan nan kafin ayi abun kunya. Yadda Uwale ta karbi Ummita to zan aikawa Yayansu ya dawo maka da danka. A'a inno na bar masa ki dena maganar nan don Allah. Ya kalli Inna ladi ki bata hakuri, ko kula shi bata yi ba taja hannun munari tana tirjewa cikin dakinta. Haka ya gaji da zama ya koma gida.
Washegari kafin azahar Inna Ladi ta aika Tani tazo da mai binta Shafa suka raka Munari birni gidan Salihu bisa umarnin iyayensu.
Haka Dijengala inji kakarta uwale ta tashi cikin kuncin rayuwa da wahala. Mahaifinta ne kadai gatanta. Tana da shekara biyu Sabuwa ta kara haihuwa. Dama ba wata kulawa Digengala ke samu ba hatta wanka sai babanta ya matsa ake yi mata. Watarana ya fita da sassafe Sabuwa ta kai ruwa bandaki a katuwar roba ta kira Hanan da Dijengala tayi musu wanka. Tana gamawa yarta tace muje in shafa miki mai tukunna. Dije wadda aka yiwa tsirara sai rawar dari take saboda sanyi tace Mama nima wanka. Wani mari Sabuwa ta gaura mata ta dauki yarta suka fita. Dije tana kuka ta taka sabulu ta zame ta fada cikin robar ruwan. Sai da sabuwa ta gama shirya Hanan bayan kusan minti goma ta dawo ta tarar da Dijengala ta kusa shidewa a robar ruwa.
FARAR HAIHUWA💰13
Da gudu ta karasa don yau akan wannan yar Mal yakubu yana iya karairaya ta. Tana dagota wani irin tari ta rinka yi har uwale ta jiyo su ta fito. To 'yar nema zaki fara sanaar tarin ne....kai lafiya sabuwa me ya faru? Wallahi Inna bansani ba. A cikin robar wanka na ganta. Na shiga uku na yau a gidan nan. Ba kuka zakiyi ba dauko gyalenki mu kaita kemis. Kila ruwa ta shaqa. Su 'ya'yan munari kamar kifaye kowa ya tashi mutuwa sai ya tsumbula ruwa.
Basu tarar da mai kemis ba dole suka wuce asibiti. A nan Mal Yakubu ya hadu dasu bayan dan aiken su inna ya riske shi. Likita yace gaskiya Mal akwai ganganci a tare daku. Yarinyar nan ba karamin kamu sanyi yayi mata ba tun kafin yau. Sannan idan ta tashi za'a sake yi mata wasu gwaje gwajen amma gaskiya a yadda na fahimta kunnuwanta sun tabu. Da kyar zata ji kamar da. Shi kam mal yakubu sarkin hawaye har ya fara. Sabuwa taci fada don ma inna ta tsaya mata ne. Karshe yace idan ta sake bari wani abu ya sami yarsa sakinta zaiyi ya hadata da hukuma.
Labarin abinda ya sami Dijengala ya sami su Inno. Hanawa sukayi a sanar da munari son kada tace zata taho tunda ta fara karatu a wata makarantar addini. Inna Ladi da ce taje gidan ta bukaci a basu ita tunda basa sonta. Bayan doguwar muhawara tace su jira shammaci daga kotu. Wannan kalami nata na karshe ne yasa Zulai ta bawa Uwale shawarar suje wurin wani malami a dauke musu hankali daga kan Dije. Anya ayi haka Zulai? Nifa gaskiya bana son inyi shirka. Haba Uwale malami ne fa ba boka ba. Ai irin malaman nan ba bokaye bane, suna da ilimin islama gashi idan kika je zaki ga littattafai da carbi kala kala. Sannan idan kika bari aka shiga kotu daurin shekaru zasu yi miki duk da tsufanki da yar kafarki. Tuni Uwale ta tsorata .A haka ta ja raayin Uwale suka je wurin malamin. Bukatarsu biyu ce. Mal Yakubu yaso Sabuwa ya hakura da abinda ya faru sannan Munari da 'yan uwanta a dauke musu hankali daga kan Dije da zancen zuwa kotun nan. Ya kasance munari ta manta ma da yar tata gaba daya.
FARAR HAIHUWA💰14
BAYAN SHEKARA 17
Cikin daga murya irin na wadanda basa ji sosai tace Inna ina kwana? Uwale ta sha kunu matsa can ni kada ki tofe ni da yawo kinzo kina min ihu a ka. Dijengala tace naam? Alamun bata ji abinda kakarta ta fada ba. Tsaki Uwale tayi tare da daga hannu lafiya nace. Murmushi tayi wanda yake kara mata kyau tace au banji ba ne. Dama ai ba jin kike ba. Ta sake daga hannu tashi ki bani wuri. To..to..to ta mike ta koma dakin su ita da Hanan da kanwarsu Zaliha.
Wata yaloluwar katifa ta nufa ta kwanta. A hankali idanunta suka ciko da hawaye. Ita meyasa bata da Umma? Ina dangin ummanta suke? Hawayen ne suka gangaro sai tari ya sarke ta. Zaliha ce ta ganta bayan ta dawo daga makaranta. Yaya Dije sannu ta dafe mata kirji. don idan ta fara tarin numfashinta har neman daukewa yake. Rashin kudi sosai yasa Babanta ke yawo da ita gidan masu maganin gargajiya, wasu suce sanyi wasu suce asma. Zaliha ta dago kan dije ta bata ruwa bayan tarin ya lafa. Ta daga murya Yaya Dije kuka kika yi ko? Tayi saurin girgiza kai tari ne Zaliha. Allah Yasa da gaske kike, bari naje na dauko mana abinci nasan yunwa kike ji ma.
Haka dokar Sabuwa ta koma abincin Hanan daban, Zaliha da Dije tare ake hada musu. Tunda Dije ta gama secondary school wadda ba wani abin kirki ta iya ba saboda rashin kunne kullum sai ta jira Zaliha ta dawo zasu ci. A cewar sabuwa kada dije ta cinye abincin. Babansu bai taba sanin wannan dokar ba don har yanzu yana so da kula da lamuran yarsa. Shekararsu goma sha biyar da baro kauyensu suka koma birni da zama. Takurawar iyayen Munari kan sai an basu Dije yasa Uwale sayar da filayenta harda gidansu ta matsa masa sai sun tashi indai ba so yake ya kulleta a gidan yari ba. Tayi mamakin yadda aikin malam bai kama su ba sai dai kuma bata kara jin duriyar Munari ba tunda tasa Yakubu ya saketa. Aikin gini da noma yake yi a haka yake ciyar da iyalinsa yake saka su a makarantar gwamnati. Tun tafiyarsu wadda basu yiwa kowa sallama ba iyayen Munari suka sanar da ita duk abinda ya faru. Tayi kuka sosai saboda tana matukar son 'yarta kuma ta kara tsanar Yakubu akan guduwa da yayi da ita. Allah Yasa ma Sadi yana wurinta.
Hanan ta fara karatu a polytechnique ta garin kano tana ji da kyau da gayu. Duk gidansu babu wanda take so kamar kakarta Uwale saboda yadda take shagwabata tana kuranta kyaunta. Duk yar yaudarar samarin da take da izinin kakarta take yi. Tana kwance kan gadon uwale tana chatting Mal Yakubu ya shigo dakin. Wani wuntsulowa tayi da sauri zat gudu. Hannunta ya rike ya dawo da ita dakin munafuka ina zuwa. Ya zaka kirata munafuka dan nan ka kiyayeni fa akan Hannan wallahi. Inna kina bata yarinyar fa. Kalli wayar hannunta abinda take saurin boyewa kenan kada na gani. Uwale tayi murmushi zancen banza ai kudin dashi na na bata ta siya dashi. Hanan tace Allah Baba ita ta bani.bari saurin rantsuwa ni tsakanina daku shawara ce. Iya abinda zanyi miki nayi na tarbiya. Allah Ya shirya.
Ficewa yayi rai a bace ya tafi dakin yaran wurin Dije da Zaliha. Baba sannu da zuwa...yauwa Zulaihatu. Taba min yayarki nasan bata ji shigowata ba. Tsinkin tsintsiya Zaliha ta sawa Dijengala a kafa ta mike a firgice. Wayyo Allah...muryarta duk ta cika gidan. Tana ganin babanta ta matsa kusa dashi. Baba kaga Zaliha ko...zan zane ta fa. Guje guje suka rinka yi a tsakar gidan yana dariya. Yaran nan biyu kadai ne suke wanke masa bacin ransa da damuwa. Sune kuma Uwale bata so don abin mamaki duk farin Sabuwa haka ta haifo Zaliha baka har tafi Dije duhu. Shiyasa uwale bata shiga sabgarsu kamar babu su a gida.
FARAR HAIHUWA💰15
Ranka ya dade ga takardun filayen guda uku aka samu a wuri daya. Alh Sulaiman Hassan ya kalli sakatarensa Modibbo nagode dan fillo. Zanyi magana da managers din sauran kamfanin sai muyi finalising project din. Modibbo yace hakan yayi ranka ya dade amma akwai sako daga wurin Hajiya fa. Murmushi yayi alamun yasan sakon Hajiyar yace nasan cewa tayi ka tabbatar yau na tashi da wuri ko? Shima Modibbo murmushin yayi ni dai umarni nake bi kuma lokaci ya riga yayi. Wai ni waye ke biyanka ne ni ko ita? Ai Alhaji da kai da kaya duk mallakar wuya ne. To naji ya fada tare da mikewa.
A hankali yake tuki don yau drebansa bai zo ba matarsa ta haihu. Karatun Al-Quran yake ji kira'ar Sheik Khaleel Husary yana bi cikin nutsuwa har ya isa gidansa a unguwar bompai ta cikin garin kano.
A falo ya tarar da ita ta gama hade rai alamun tana fushi dashi. Mata ne biyu zaune tare da ita. ko da ya gaisheta da kyar ta amsa masa shima yasan yayi laifi bai matsa mata ba yayi hanyar bene tace cikin fushi Sulaiman ina zaka je kuma? Umma zan canja kaya ne na dawo. To kayi sauri yaran kawata ne suka zo gaisheni shine nace su jira kazo ku gaisa. To kawai yace a ransa kuwa harda dariya...umma kenan ta zama matchmaker karfi da yaji ita a dole sai yayi aure a wannan shekarar. Shima kullum yana adduar samun ta gari yasan kuma Allah mai jin rokon bayinSa ne.
Wanka yayi yasa kananan kaya ya sauko. Yana zama Umma ta mike to bari na duba abinda ake dafawa. Yasan so take ta basu wuri ya ce to kawai. Tana tashi dayar wadda take ta yi masa kirikiri da ido tace Yayanmu ni sunana Ainau wannan kuma kanwata ce Bilkisu. Ko kallonsu baiyi ba don basu yi kama da masu kunya ba ya zaro kudi a aljihunsa ya mika musu ga kudin mota nice meeting you. Sai anjima muje nasa dreban Umma ya kaiku gida. Ainau ta bata rai ai Hajiya tace mu jira zaka kaimu da kanka idan ka dawo saboda kaga gidan. Ashe ma doluwa ce yarinyar ya fada a ransa. Kinga naji ciwo a hannun bari a kaiku. Bani number dinki zan kiraki musamman. Kanwar tace nifa? Itama karbar tata yayi yana so suyi su fita kafin Umma ta dawo. Sai da yaga fitar motar daga gate din gidan ya dawo ya zauna. Muryar ummansa yaji tace Sulaiman ina su Ainaun suke. Ai sun tafi wai sauri suke yi...amma yaron nan baka da kirki. Wai so kake na mutu banga jika na ba shekarunka talatin da shida fa...jin ta fara shakar hanci yasan kukan blackmail ne ya tashi. Kiyi hakuri Ummana na sami mata ina jira mu gama daidaitawa ne. Ta washe baki hakoran makkanta suka bayyana. Da gaske Sulaiman? Da gaske Umma..to ai da kayi magana da wuri bazan kira yaran nan ba, dama nima duk basu yi min ba. Yadda tayi maganar yasa shi dariya sosai.
Modibbo da abokinsa Mal Yakubu suna zaune kofar wani gida da su mal yakubu ke aikin ginawa yace mutumina Alhajin kamfaninmu ya sayi wasu filaye manya guda uku. Ban dai san abinda zai gina a wurin ba amma naga so yake ayi ginin da wuri. Zanyi masa magana akan ka ka samu shiga cikin masu yin aikin. Nagode Modibbo Allah Ya bar zumunci. Wallahi kudin karatun yaran nan da ciwon Dije sune suke damuna. Kada ka damu in sha Allah zaka sami wani abin yanzu don Alh Sulaiman akwai kirki. Haka suka zauna suna ta hira har laasar tayi suka tafi gida tare.
FARAR HAIHUWA💰16
Hannu yaji ya sakalo masa wuya ta baya. Daddy oyoyo...tashi yayi ya daga Ammar sama yana ta dariya. Umma ta fito ni kun cika min gida da ihu abinda kuka iya kenan. Dariya suka sake yi mata Ammar yace Daddy dazu mamana tazo kafin ka dawo daga office. Umma ya kalla tace Ammar je ka daki ka dauko wa daddy tsarabar da tayi maka. Yana fita tace zuwa tayi ta sanar dani ta sami mijin aure. Ai gara tayi auren ta dade shekara shida ai ba kwana shida bane. Sulaiman yace Umma Allah Yasa dai ba fushi kike dani ba akan rashin aurenta. Gyara zama tayi ko kadan duk uzurin da ka bani na karba. Idan ka kai mata Ammar ranar jumaa sai kaji ko waye mutumin.
Alh Sulaiman Hassan shine da na biyu a wurin Haj Bintu. mahaifinsa babban dan kasuwa ne kuma yana da kamfanin yin kafet har uku a kasar. Shekarar Sulaiman ashirin da daya baban nasa ya rasu bayan yasha jinya yayansa Yusuf ya cigaba da kula da kamfanin baban. A lokacin da yake masters dinsa a fannin aikin banki , Yusuf ya rasu sakamakon hatsarin mota da yayi. Ya bar matarsa sakina da ciki wata biyar. Bayan ta haihu ne Umma tayi ta kokarin hadasu da Sulaiman yaki yarda a cewarsa bazai dena kallonta a matsayin matar wansa ba. Shekaru shida kenan sai yanzu ta sami wani zata aura.
Saboda matsin layin daga can baya Sulaiman yayi parking motarsa shi da Modibbo suka taka da kafa zuwa kofar gidan Mal Yakubu. Kwata ce a kofar gidan dole suka shiga daga dan zauren waje inda Uwale ke kiwon tumaki. Banda wari da zarni babu abinda ke tashi a wurin. Sulaiman ya gimtse fuska. Modibbo sarai ya gane warin ke damunsa yace yallabai kayi hakuri shiyasa nace ka zauna a mota na kira shi.
Ba komai Allah Yasa ya fito yanzu dai.
Wata kyakkyawar yarinya ce ta fito fara tas harda dan karin mai. Cikin yanga take tafiya. Gaba daya hankalin Alh Sulaiman ya koma kanta. Baba yace yana zuwa ta fada ba tare da tayi musu sallama ko gaishe su ba. Ciki ta koma tana taunar cingam.
Mal yakubu ya fito ya gaishe da Alh Sulaiman sannan ya gabatar da kansa. Alh Sulaiman yayi masa bayanin wurin da filayen suke ya kuma bukaci yazo kamfani ya same shi washegari.
Ihun da suka ji yasa su yin shiru Dijengala ta fito da gudu tana kuka. Murya can sama tace Baba kaga Mama ta hanani wanka yau ma wai zan karar da ruwa. Kaji yadda nake tsami kuwa...matsawa tayi gabansa tana daga masa hannuwanta har gashin hammata Alh Sulaiman yana gani. Kuma fa jinin wata na yazo tun jiya . Subhanallahi Dije sauke hannun mana ya kama hannunta zai koma cin gidan da ita. Tirjewa tayi Baba dukana fa zata yi kuma kullum Yaya Hanan tana yi da Zaliha. Duk kunya ta kamashi ya daga murya don taji abinda yake fada...muje nace zan mata magana. Burinsa kawai su koma cikin gida. Sai lokacin taga mutane tsaye...lahh baba modibbo sannu da zuwa. Sai ta rike baki au...duk kunji abinda na fada ko? Wayyo kunya ta dafe kai tare da komawa cikin gida. Alh Sulaiman kuwa dariya ce ta kwace masa ganin yadda Dije take baragada a gabansu. Sai dai fa akwai wari dan kare.
FARAR HAIHUWA💰17
Wani murmushin ya sake yi shi kadai Umma ta jefe shi da pillow din kujera kai ni dariyar me kake yi kamar kwancen hauka....wata dariyar ya sake yi sannan ya bata labarin Dijengala kurma. Itama dariyar tayi maimakon ka taimaka mata shine kake dariya. Ni mubar wannan zancen dai ya sunan yarinyar da kayi min zancenta ne? Ga mamakinsa sai yaji yace Hanan.
Daren ranar tunaninta ya rinka yi. Tana da kyau mai daukar hankali gashi da gani tana da tsafta ba kamar Dijengala ba. Wani murmushin ya sake yi da ya tuno yadda take magana. Daga nan har yayi bacci tunaninsa yana kan Dije yana dariya.
Ranar litinin duk ya kagu modibbo ya iso. Yana zuwa kuwa tambayarsa tayi ko anyiwa Hanan miji. Modibbo yadan yi turus...Hanan dai yar abokinsa ce amma ko kadan bata da hali. Ranka ya dade ba ayi mata miji ba a iya sanina. To ka sanar da mahaifinta idan ya amince zan nemi aurenta. Modibbo ya nuna farincikinsa a fili amma ba don yadda Dije ta tashi ba sai shirme da shiririta ga lalurar kurumta da ita zai so Alhajin ya nema.
*******************
Rana duk ta dami Hanan a kofar banki inda take jiran kawarta. Wata mota take ta kallo, ba karamin kyau tayi mata ba...duk mai motar nan ko ba'a fada ba mai kudi ne kuma mai kyau. Tayi dan tsaki ita kyau ma bai dameta ba indai akwai kudi. Tana zaune a wurin wani matashi ya fito ya bude motar. Gaba daya ya tafi da hankaliñta ta bishi da ido. Kana ganinsa kaga kudi don yawan shige shigenta tana gane mai kudi tana gane yaron mai kudi. Wannan matashin kam shine da kudin. Tashi tayi ta kade skirt dinta tayi saurin zuwa gaban motar inda yake shirin rufe kofa tace Alhaji kwana biyu. Ya dan dago kai a dakile yace ya kin sanni ne? Tayi baya yi hakuri sai naga kamar wani da na sani ne. Sai kashe murya take tana magana ciki ciki. Ya bata rai bashi bane to...matsa na rufe kofar. Kafin ta gama matsawa ya bugeta da kofar ya figi motarsa. Kafin ya bace ta gama haddace numbar motarsa.
FARAR HAIHUWA💰18
Kawarta Hajara ce ta fito jaka cike da kudi. Sorry Hanan na barki jira ko? Gaskiya da mita zan miki amma na fasa. Wani kamu nayi mai kauri. Hajara tace haba a yana ina? Hanan ta fada mata yadda suka yi. Amma zancen gaskiya kawata yayi min akwai kudi. Ji nayi kamar kudin jikinsa yana kirana. Shegiya uwar son kudi nasan wannan mai cangala kafar zaki kaiwa. Allah sarki innata tafi kowa kaunata. Ni ba wannan ba Hajara ki rakani gidan Babba mana. Akan mutumin nan sai anyi aiki.
Dayake halinsu yazo daya shiyasa kullum a makaranta tare suke. Hajara da Hanan suka wuce gidan Babba wani malamin tsibbu. Don yanzu bin malamai harda yan mata. Allah Ya kara shirya mu. Bayan dukkan bayani Babba yace Hanan kin san sunansa? A'a amma ga numbar motarsa, ka taba yi min aiki akan wannan wawan malamin da numbar waya ai. Ba damuwa Hanan ga wanan turaren ki saka kan garwashi sai ki rubuta numbar motar a takaddu goma ki rinka dorawa akan wutar har su cinye duka. Sai ki lazumci zuwa wurin da kuka hadu na kwana goma. Idan baki ganshi ba to motar ba tasa bace. Godiya tayi sosai tace idan ciniki ya fada zaka ganni.
Bayan kwana uku Modibbo ya sanar da Mal Yakubu bukatar Alh Sulaiman. Murnarsa bazata misaltu ba ya sanar da Uwale. Burinshi dama tayi aure ya gaji da sintirin da samari ke yi masa a kofar gida. Sabuwa ma tayi murna har ta sanar da babarta Zulai. Cikin dare ta bawa mijinta shawarar ya aurar da Dijengala. Banda abinki Sabuwa ina Dije take da saurayi. Tayi wani murmushin keta...wani kurma ne dan uwan Zainab makociyarmu. Tace a kauyensu yake Kura. Hade rai yayi dakata malama ni 'yata bata gama kurmancewa ba kinji ko. Ki rike abinki rabonta na tafe. Kuma dama ina son yi miki magana Allah ranar da kika sake hanata ruwan wanka zaku yini a gidan nan ba ruwa. Yar hirar tuni ta watse ya juya yayi kwanciyarsa.
Gari na wayewa cike da zumudi Uwale ta sanar da Hanan zancen Sulaiman. Ta wani harareta jiya tasha uban hayaki akan wani yau a kawo mata zancen wani Alh Sulaiman. Kinga Inna ki bar maganar nan ina da wani. Haba Hannan mutumin nan fa kudi gareshi sosai. Mafarkina a kanki ne zai tabbata. Hanan ta wuce zata shiga wanka. Kinga Inna ki bar maganar nan ku bashi Dijengala ko Zaliha. Auzubillah uwale ta fada tana tofar da yawu. Dije ai ai musaki irinta. Yarinya ga baki ga muni.
FARAR HAIHUWA💰19
Hanan tayi sati daya tana zuwa bankin da suka je da Hajara tun safe har sai sun tashi amma mai motar bai dawo ba. Rai a bace ta koma gida duk ta kusa gama kashe kudin hannunta a hawa motar zuwa banki.
Dakinsu ta shiga zata cire kayanta tayi wanka Dije ta shigo tana waka da karfi. Hakan ya kara batawa Hanan rai ke rufa min baki banza kawai. Ta fice tana tsaki. Babanta ta gani a kofar kitchen yana magana da Sabuwa...yauwa zo hanan dama zancenki muke yi. Ta turo baki gaba ta karasa gabansa ta tsaya. Nasan an fada miki maganar Alh Sulaiman ko. Wanda kuke aikin gini dashi baba? Eh ya amsa mata. A zuci tace tabdi magini zan aura? Allah Ya kiyaye, itama Mama tsautsayi ya kawota gidan nan. Mal yakubu yace dama tafiya ce ta kamashi amma ya dawo zai zo yau da daddare inji modibbo. Uhmm tace ta wuce bandaki. Wallahi bazai sameta a gida ba ma. Me zatayi da talaka.
Haj Bintu tana ta kallon yadda Sulaiman ke shirin fita daga dawowarsa ko abinci bai ci ba. Ina zaka ne don nasan wannan shigar bata zaman gida bace. Hular hannunsa ya gyara Umma gidansu Hanan zani amma da Ammar zan tafi saboda zan kaishi aski. Wato ka dawo zaka nuna min ban iya kular maka da danka ba ko? Yana dariya ya bata hakuri. To ina tsarabarta ko haka zaka tafi? Mata fa sai da ihsani. Zan biya na siyo wani abun a hanya. Hannun Ammar ya kama suka tafi yana ta yi masa hira.
Hanan ta rasa yadda zata yi ta fice daga gidansu tunda babanta yaki fita tun safe. In ba rashin aikin yi ba kakkarfan mutum kamarsa ya zauna a gida wuni guda....tayi tsaki. Zaliha tace lafiya. Hararar ta tayi ban sani ba ta bata amsa tare da fita daga dakin. Mal Yakubu na fita zuwa masallaci sallar magriba ta fice ba tare da sanin kowa ba.
Alh Sulaiman yana dosar gidan ya fara jin warin kwatar kofar gidan. Shifa harkar warin nan baya kaunarta. Ya rasa dan aike gashi bashi da numbar wayar kowa a gidan.Ammar ya tura ciki ya sanar da zuwansa. Yaro ya shiga kai tsaye dakin da ya hango haske ya nufa. Uwale ce da Sabuwa suke kallo yace salamu alaikum wai daddy na yace ya zo. Sabuwa ta kalli dan kyakkyawan yaron kai kuma daga ina wa ya turo ka? Mal Yakubu ya shigo yace dan Alh Sulaiman ne mai son Hanan. Kirata Sabuwa yana jirantaa soro.
FARAR HAIHUWA💰20
Sau uku ta kira taji shiru. A zaune ta tarar da Dije tana gyangyadi kafin Zaliha ta dauko musu tuwo. Shureta tayi da kafa ke kurma tashi...a firgice ta tashi tace mama me ya faru? Ta dungure mata kai tare da rage murya ubanki ne ya faru. Dije ta bata fuska tana nuna kirjinta ubana? Ubana?? Sai hawaye...ke yi min shiru munafuka ana magana sai kiyi ta kallon bakin mutane ina Hanan? Dije tace ta fita tun dazu. Kai yarinyar nan zata ja min masifa ta koma daki ta fadaw Mal yakubu.
Ransa yayi matukar baci gashi yar wayar tasa ma ba kudi bare ya kirata. Uwale tace yarinyar nan neman tona min asiri take ga wayata kirata. A kashe suka ji wayar. Bari na fada masa kawai ,ita kuma yau tamu ce ni da ita.
Jin Zaliha bata dawo daga dauko musu tuwo ba Dijengala ta duba kitchen bata ganta ba ga yunwa yana cinta. Ita kuwa Zaliha cikinta ne ya kada ta tafi bandaki. Wata tsohuwar naira ashirin ta dauko a kasan akwatinta ta saci jiki zata je siyan wainar fulawa a gidan Zainab makociyarsu. Tana saka kafarta a soron aka dauke wuta, saboda duhu hannunta take mikawa kamar makauniya tana neman hanyar fita, wani mulmulallen abu mai dan gashi gashi taji ta shafa ta tabbatar ba kan daya daga tumakin Sabuwa bane. Ammar data tabawa kai ihu ya saka. Daddy kamani naji an taba min kai. Sulaiman yace ina zuwa Ammar wayata nake nema. Dije sake taba kan tayi don ta tabbatar da abinda ta taba, gashi tana jin kamar maganganu amma ta kasa gane me ake fada. Ihu tasa iya karfinta wayyo Allah baba nayi gamo. Sulaiman tuni ya gano muryar yar kazamar yarinyar nan yace ke rufa mana baki yana neman hannun Ammar su fita. Ta soma kuka Al'Quran naira ashirin ce a hannuna waina fulawa zan siyo a gidan Zainab yunwa nake ji. Gashi don Allah kada ku mayar dani kaza ko doya. Ba shiri sulaiman ya soma dariya...hannun dansa ya kama. Yana jin yadda Dijengala take tsalle da ihu. Mal Yakubu ne ya iso soron da yar fitila. Shima bai kula da su Sulaiman ba don ya zata sun tafi. Dije dena ihu nine...tana ganinsa tayi saurin matsawa kusa dashi tana magana da karfi, baba aljanu ne suke son bude min ido, dansu suka turo min shegu. Kul kike zagi dije...shima baba zuciyarsa ta kusa bugawa daya ji ance daddy mu tafi. Sai a hankali ya gane Alh Sulaiman ne da dansa.
FARAR HAIHUWA💰21
Da kyar ya iya tsayar da dariyarsa yace Mal 'yar nan taka tana da abin dariya. Ai nima na tsorata don nayi tunanin kun tafi. Ammar ya nuna takalminsa ne ya kwance na tsaya daure masa sai aka dauke wutar kuma ina tunanin wayata tana mota. Sake sallama suka yi kafin Sulaiman ya gama fita yaji mal yakubu yana tambayarta ina zata.. wallahi baba yunwa ce kuma zaliha bata kawo abincin ba, dama wainar fulawa zan siyo ta ashirin. Dariya yayi haba Dije wainar ashirin ai sai da kiyi kuskurar baki da ita. Me kace baba? Banji ba. Muje na baki nawa abincin kici a daki kada sabuwa ta gani. Daddy mu tafi mana wari nan. Sai a lokacin sulaiman ya dawo hankalinsa yaja hannun Ammar suka fita bakin layin inda yayi parking motarsa.
****************
Ashir ya rasa abinda ke masa dadi. Tun washegarin zuwansa banki zuciyarsa ke masa radadi ya rasa dalili. Ji yake kamar ya koma bankin ya nemi yarinyar da ta yi masa magana amma shi ko fuskarta ma bazai iya tunawa ba don bai kalleta da kyau ba. Wata biyu ya rage bikinsa amma yan kwanakin nan baya son ko jin sunan matar da zai aura. Dama dai auren baya gabansa don shine na uku ma. ba ya dadewa da mata suke rabuwa, hakan na damun yan uwansa shiyasa wannan karon babansa ya yanke shawarar hada shi da yar kaninsa da mijinta ya rasu shekaru shida da suka wuce, wato sakina mahaifiyar Ammar. Gidansu Ashir suna da rufin asiri dai dai gwarwado. Lokacin da ya fara aikin kwangila ga aikin office shine kudi suka zauna masa sosai. Kasa nutsuwa yayi karshe ya yanke shawarar zuwa bankin a daren bayan yayi magriba a kofar gidansu.
Hanan na sauka daga adaidaita sahu suka hada ido da mutumin da take ta nema. Gabansa ne ya fadi yana ganinta. Banda kyawunta wani yanayi ya shiga mai wutar fassara. Idan bai auri yarinyar nan ba rayuwarsa tana cikin matsala. Har wani gumi ke keto masa. Karasawa yayi inda take ba tare da yayi mata magana ba ya mikawa dan sahu dubu daya yace mata zo mu karasa bakin motata. Ba musu ta bishi...lallai aikin Babba yayi kyau.
FARAR HAIHUWA💰22
Bude mata yayi ta zauna a seat din gaba. Shima yana zama yace me ya fito dake a daren nan? Ta rausayar da kai tana kare masa kallo, ga kyau ga kudi.ready made kenan..kai ya kamata nayiwa wannan tambayar. Hmm ina jin abinda ya fito dani ne ya fito dake. Me kenan ta tambayeshi ciki da jindadi. Yana kallonta yace tunaninki mana. Duk kin hanani sakat...ina tunanin kema hakan take a wurinki. Ni fa kudi nazo dauka ba wurinka nazo ba. To fitar min daga mota indai hakane. Tsoron kada garin jan aji ta rasa shi yasa tayi saurin cewa wasa nake maka. Nima ka hanani nutsuwa tun ranar da muka hadu. Yaji dadin amsarta...ni sunana Ashir Sani. Ina aiki a NNPC sannan ina harkar kwangila sosai. A takaice dai i am a very busy man. Ina ruwanta da yawan aikinsa indai akwai kudi. Ta fada masa nata sunan daga nan hira suka rinka yi kamar sun dade da juna. Ganin tara ta wuce yace muje na kaiki gida.
Alh Sulaiman na fitowa daga layin gidansu Hanan ya hangota cikin motar wani. Ina taje a daren nan ya tambayi kansa. Motar na kara matsowa yaga kamar yasan mai tukin amma ya kasa tuna ko waye. Bai kawo komai a ransa ba ya tafi gida.
Cikin sati biyu soyayya ta kullu sosai tsakanin Ashir da Hanan. Ta sanar da uwale da sabuwa komai game dashi. Tuni ta sace zukatansu bare da suka ga irin hidimar da yake mata. Mal Yakubu dai ya nuna rashin amincewarsa. A cewarsa bazasu mayar dashi karamin mutum ba. Ya riga ya amsawa Alh Sulaiman har yace zai turo iyayensa don baya son a dauki lokaci. Uwale tace to dan nema mai toshe kofar arziki. Shi Sulaimanun nawa ya taba bata tunda yazo. Inna ki dena koyawa yarinyar nan son kudi, zuwansa uku fa kullum ba ta gida. Yau idan ta dawo sai naci mutumcinta. Shegen yawo kamar kaza. Uwale ta sha kunu bana son irin haka fa, ka manta tana karatu ne? Ni dai na gama magana yarinya Ashiru zata aura. Jiya da ya shigo dubu goma ya bani. Ni Uwale da dubu goma tawa ta kaina. Ka sallami wannan abokin ginin naka don bazan bashi jikata ba.
FARAR HAIHUWA💰23
Abokin gini kuma Inna? Ni da na fada miki gini zanyi masa yana da kamfani. Sabuwa da tun farko bata yi magana ba tace haba Malam wai kai a dole sai ka nuna baka son yarinyar nan ne? Ya arziki na binmu kana sa kafa kana shurewa. Babu wanda ya isa yayi mata dole. Wanda take so zata aura. Idan kuma dole ne sai ks bashi Dijengala ai itama mace ce. Inna Uwale ta tuntsire da dariya...wa yaga barahaza. Ba yadda ya iya dole ya kyalesu idan suka hade masa kai don baya iya musu da Inna Uwale. A zuciyarsa ya gama yanke shawarar sanar da Modibbo ya bawa Alh Sulaiman hakuri. Dama can ba sa'an auren yarsa bane shima don yaga kamar auren zai hanata yawo ne.
Alh Sulaiman yana mamakin yadda duk lokacin da yaje baya samun Hanan kullum sai ace masa bata nan, gashi Umma duk ta kwallafa rai. Shi kanshi yana son ya kara ganin kyakkyawar fuskar Hanan din. Yarinyar akwai class. Yana dawowa daga office ya shirya ya tafi gidansu da yamma. kila don saboda zuwan dare yake shiyasa baya samunta. Yau tararta zaiyi kafin ta fita. Yana tuki Dijengala ta fado masa a rai. Shi kadai yayi murmushi Allah Yasa itama na sameta...a ransa har ya gama shawarar idan yau auri hanan zai ce ta taho da kanwar tata.
Yau ma can baya ta ajiye motarsa. Sabuwar benz ce da masu kudi ke yayi ya shigo lokon a kafa. Farin yadi ne a jikinsa mai bula bula. Wandon da shafi amma babu a rigar, ana ganin farar vest din dake ciki. Takalminsa da hula duk ruwan toka ne. Yayi kyau sai kamshi ke tashi duk inda ya wuce. Bai ankara ba yazo daidai kwatar kofar gidan Mal Yakubu yaji an kwala ihu sai ruwan kwata ya gani ya fallatso masa ko ta ina a jikin kayansa harda gefen fuskarsa. Ransa ya gama baci sosai saboda shi mutum ne mai matukar kyankyami. Dijengala ya gani kafarta daya a cikin kwatar babu ko mayafi a jikinta tana kuka. Ganinsa a tsaye yasa kukan ya karu ta soma bashi hakuri da karfi. Don Allah kayi hakuri ban sani ba. Inna ce ta biyoni da bulalar doki. Kafin yayi magana wata dattijuwa ta fito daga gidan da ke kusa dana su Dije. Daga murya tayi yadda Digen zata ji...me ya faru Digengala? Ta sake wani sabon kukan sannan ta fita daga kwatar ta karasa wurin matar. Gwaggo, Inna ce tace yau bazanci abinci ba sai na debo ruwa bokiti goma. Kuma fa na debo shida amma yunwa nake ji. Tace na sa baba yaki siyo ruwa saboda sun hanani na wanka jiya daya fita. Gwaggo taja hannunta kiyi hakuri kinji yar albarka shigo kici abinci kiyi wankan. Ta kalli Sulaiman wanda ya zuba musu ido. Alhaji shigo kaima kuma kayi hakuri.
Ya kalli tsohuwar ba damuwa? Haba yaro ni da 'ya'yana biyar ne a gidan nan babu mace ko daya sai matar babban. Kazo ka dan gyara jikinka. Suna shiga daga bakin kofa ya tsaya aka bashi buta ya dauraye kafarsa yana ta dage hanci. Kadan ya rage burinsa ya koma gida kawai. Yana ta kallon yadda Dije ke cin abinci da sauri da sauri. Yace don Allah ina da tambaya gwaggo. Ina jinka ta amsa. Wai ita yarinyar nan wace ce ita? Kamar jira take ta bashi labarin duk abinda ta sani game da Dijengala da wahalar da Sabuwa da uwale ke bata. Sosai ya tausaya mata bata da wata damuwa sai ya cikinta. Yayi godiya zai fita Gwaggo tana yiwa Dije waka. Dijengala ta maigari, ba auren talaka ba. Yana bakin kofa suka ji ance sai auren musaki ba, kurma irinta.
Inna Uwale ce ta hau kan wata katuwar bambu ta ruwa da aka kifa daga gidanta. Sabuwa ta riketa ta tsaya don kar ta fada ta leko ta katangar da ta hada gidanta dana gwaggo. Sulaiman har dan tsorata yayi sai kuma ya tsaya yana jin tijara irinta Uwale. Dije tuni ta tashi daya kan kwanon tuwon ta koma bayan gwaggo ta buya. Zaki shigo gidan ki same ni ne 'yar banzar yarinya, waye bawanki da zai debo ruwan. Gwaggo tace Ke dai Uwale kinji kunya wallahi...idan zaki shekara kina nunawa yarinyar nan tsana bazaki taba canjawa kanki suna a matsayin kakarta ba. Kuma wallahi idan kika sake min leqe da wannan shanyayyar kafar taki sai na tsire miki idanu. Cikin fushi tace ni kike fadawa haka...wallahi zan hadaki da hukuma su shiga tsakaninmu. Makotaka ai ba hauka bane duk kin samin ido inji uwale. Gwaggo tace anji kunya dai ace danki ma hakuri yake da halinki, duk kin bata masa gida da tashin hankali. Kin rabashi da matarsa da yake so kin hada shi da wannan makirar. Shewa uwale tayi kamar ba tsohuwa ba. Ai na isa ne.
Sabuwa ce taji cizon cinnaka a kafa ta saki Uwale ji kake timmm ta fado tana ihu. Gwaggo tace Allah Ya kara kadan ma kika gani.
Shi dai Sulaiman tunda yaji maganganun wanda basu san ma yana kofar soron ba sai tausayin Dijengala mai cin tuwo ya kamashi
FARAR HAIHUWA💰24
Yana isa gida Ammar ya tare shi a bakin kofa...hmmm daddy wari. Umma dake zaune tana yanke farce tace daga ina haka. Itama ta kama hanci kai me ya sami kayanka. Ina zuwa umma bari na gyara jikina.
Bayan yayi wanka doguwar riga yasa ya sauko kasa. Yana zama ya fara yiwa Umma hirar dijengala. Yadda yake bayanin cike da nishadi kamar ba shi aka watsawa kwata ba. Umma tace wai ni Sulaiman kanwar kake so ne ko yayar? Murmushi yayi Umma yar nake so mana. Ita wannan Dijen zanso ki ganta. To ai yadda kake fada kamar babar hanan din ke takura mata. Ba don yar ka fara nema ba ai da sai ince ka nemi Dijen don naga tafi burgeka. Ahh haba umma kurma ce fa. Ta rike baki to sai me Sulaiman? Kurma ba mutum bace? Ni nafi son irin auren nan da zai kasance taimako ga wani.
Tun da Umma tayi masa magana sai kawai hankalinsa ya rabu biyu. Tabbas sau biyu yana tarar da rigima da Dije akan ruwan wanka. Kana ganinta kuma sam babu gyara. Yasan a kalla zata kai shekaru ashirin. Da wannan tunanin ya jira litinin tazo. A office ya sake yiwa modibbo tambayoyi akan Hanan. Wannan karon gaskiya ya gaya masa game da halayyarta. Kuma a yadda babansu ya fada min jiya wai kakar ta zata kaima aikin gini kake yi shiyasa suke son a bawa wani. Mal Yakubu har kunyar ka yake ji saboda yadda take ficewa daga gidan kafin kazo. Hmm wato sun dauka talaka ne shi yake fada a ransa. To idan ba damuwa modibbo ka sanar dashi zanzo gidansa zuwa karshen sati akwai maganar da zamuyi. Modibbo fata ya rinka yi Alh Sulaiman ya nemi auren Dije.
Alh Sani ya kalli dansa Ashir..yanzu da gaske ka fasa auren sakina? Ashir me kake son mayar dani ne. Haj Lami tace kaga duk wancan auren kai kake zaba masa kila shiyasa baya karko wannan karon don Allah kada kayi masa dole. Ai dama da saninki yake wannan wulakancin. Yanzu meye aibun Sakina? Haj tace bazawara ce fa. Ga budurwa ya samu son kowa. Har hotonta nagani. Alh Sani yace shi ma ai bazawarin ne...bazan tilasta masa aurenta ba kada ya bata mana zumunci amma wallahi Ashir idan ka kara sakin mace zan maka ba dadi. Shashasha wanda bai san mutumcin kansa ba. Shi dai Ashir ko tak bai ce ba ya tashi ya tafi gidansa. Me zaiyi da wata Sakina ana zaune kalau. Yadda son Hanan ke ci masa zuciya baya fatan a wuce wata daya bata zama matarsa ba.
Yau Alh Sulaiman da abokinsa ya tafi gidan Mal Yakubu bayan sun yanke shawara shi da Ummansa. Umar yace yanzu Sulaiman har lokon nan ka zo neman aure? Wannan yarinya ta ciri tuta. Yayi dariya sai ma ka ganta mutumina. Ai na iya zabe.
Goruba take ci a kofar gidan Gwaggo ita da kawarta. Kawar ce ta fara hango su Sulaiman tace ke Dijengala kinga wasu yan gayu can. Dije na ganin Sulaiman ta gane shi. Al'Quran shine mutumin dana watsawa kwata. Tashi mu gudu dan sanda ya dauko min. Na shiga uku.
Da gudunta ta tafi zata shiga gida ta kira babanta ya basu hakuri don taga kamar kayan jikin abokinsa na yan sanda ne. Bakaken kaya ne shirt da wando ne. A kokarin gudun ne dan katakon daya raba kwatar gidansu ya rufta da ita ta sake yi masa kwalliya da kwata. Rasa bakin magana yayi don takaici yana tunanin fasa abinda ya kawo shi. Ita kuwa Dijengala ta gama tsurewa don tsoro ta bare baki tana kuka, muryarta a sama.
FARAR HAIHUWA💰25
Subhanallahi, Sulaiman kaga wata mahaukaciya. Zo mu koma ka canja kaya sai mu dawo ko anjima ne ko gobe. Kamar ba dashi Umar yake magana ba, hankalinsa yana kan Dijengala da take ta ihu. Dan matsowa yayi kusa da ita yi shiru Khadija ba kama ki zanyi ba. Hannu tasa tana share hawaye tace lah kaima kasan sunana na makaranta ashe. Ita dai abokiyar cin goruba tuni ta shige gidansu. Yace na sani yanzu dai fito daga cikin kwatar nan. Ta kalli jikinta tabdi yau na karar da nawa ruwan wankan sai da muje gidan Gwaggo mu diba a rijiya. Ka tuna inda muka je rannan???
Yayi murmushi cike da dauriya don wani amai ke taso masa saboda yadda jikinsa ke wari.
Umar yace wai Sulaiman a nan zamu biyewa wannan mahau....dakata fa Umar ya tsayar dashi. Meet my wife to be. Dan murmushin fuskar umar ya bace...are you serious? Cike da nishadin da ke baibaye shi idan yaga Dijengala kurma yace Allah da gaske nake. Dije dake tsaye a gefe tace zo muje mana kafin kuda ya fara bin mu. Suna tsallakowa tace wai kuwa kai ba dan yankan kai bane? Umar har kusa faduwa yayi da jin abinda ta fada. Sulaiman yace meyasa kika ce haka? Ta dan tabe baki naga ka nace wa gidamu ne...ance da haka kuke farawa sai kawai ku sace mutane. Umar sai kallon ikon Allah yake yadda take magana ko a jikin Sulaiman. Yace wurin babanki nake zuwa bana satar mutane. Au to har hankalina ya kwanta...ta jefar da kwallon gorubar hannunta. Ai wallahi da niyata muna shiga gidan gwaggo nayi maka ihu, kasan duk 'ya'yanta maza ne. Sai su kamaka a dora maka taya a cinna maka wuta. Dariya sosai Sulaiman yake Umar na kallonsa...anya kalau kake kuwa sulaiman? Tana zancen sawa a konak kana dariya? Kuma kuna ta daga murya kamar kurame. Sulaiman ya rage murya kurmar ce ai. Isn't she cute?
Suna shigowa soron gidan ta fella da gudu. Zasu raina mata wayo sun zata bata gansu ba suna wani magana a hankali. tana shiga tasa ihu gwaggo ta fito da sauri...lafiya Dijengala? Har haki take tace Gwaggo ashe mutum min nan mai satar mutane ne? Yau ma ya dawo ina su Yaya Tajo? Ayi gangamin kama su don yau harda wani kato yazo.
Sulaiman da umar suna jin ta. Ya rinka dariya Umar yace Allah tafiya zanyi kada a kona ni daga rako ka zance.
FARAR HAIHUWA💰26
Gwaggo ta dauko tabaryarta tayo hanyar soro. Tana ganinsu tace au Alhaji kaine...kaji shirmen Dijengala ko. Wallahi duk na zata da gaske take. Kallon jikinsa tayi...ba dai yau ma kwatar kuka fada ba? Murmushi yayi yace bata kula bane ta fada ciki.
Daga ciki suka jiyo Dije tana cewa ba dai sun tafi da Gwaggo ba. Na shiga uku me zan fadawa 'ya'yanta. Shigowarsu ta gani ta saki baki na tuba don Allah ku yi hakuri kaga ni bana ma ji sosai kaina bazai yi kudi ba. Gwaggo tace rufa min baki sarkin surutu.dauko musu ruwa a buta. Kema ki je ki gyara jikinki.
Bayan sun kammala gwaggo tace kai kuma kullum kuka hadu da Dije sai tayi maka wanka da kwata. Ba komai Gwaggo dama mahaifinta nake son gani. Bari naje nayi masa magana da kaina to, kasan halin yarinyar nan ina iya turata taki dawowa.
A wulakance su Uwale suka gaisa da gwaggo tace wurin Mal nazo. Sabuwa tace bacci yake yi. Mal yakubu ya fito suka gaisa. Tace dama kayi bako ne shine babu dan aike nazo yi masa sallama da kai. Uwale tace haka dai aka iya gulma da sa ido. Gwaggo bata kula ba suka fito waje...mal yakubu bakon yana gidana fa. Yace sunansa Alh Sulaiman. Mal yace subhanallah wallahi har kunyarsa nake ji. Ya sanar da ita yadda suka akan maganar Hanan. Gwaggo tace to Allah Ya kyauta muje sai kayi musu bayani.
Umar ne ya gabatarwa mal Yakubu bukatarsu game da Dijengala. Sulaiman yace baba kada kaga kamar ina maka yawo da hankali. Naga kamar Hanan din tana da wani ne shiyasa. Tamkar an mishi albishir da kujerar makka yace da gaske kake Alhaji? Kai zaka auri Dijengala. Sulaiman yace in har ka amince. Na fara sanar da kai ne don neman izini kafin na turo maka iyayena. Farincikinsa baya misaltuwa yayi godiya sosai. Umar ya bashi dubu ashirin yace baba ga wannan mungode.
Suna tafiya Mal ya dauki kudin ya bawa gwaggo ajiya dama ya saba shawara da ita. Yace yanzu zan sami nutsuwar amsawa wanda yazo neman auren hanan. Dama saboda na riga na amsa tun farko ne. Gwaggo tace ai gara tayi auren saboda Uwale kara bata ta take yi. Haka suka yi ta yan shawarwarinsu sanan ya kira Dije ta fito daga daki suka koma gida.
Ashir ya dage sai shirye shirye yake. Anyiwa gidansa sabon fenti an gyara ko ina. Dama ya kusa gama hada lefen Sakina saboda haka abinda ya rage ba yawa. Ya dai kashe kudi sosai don duk abinda Hanan tace ta zauna. A dan lokacin da suka hadu ya siya mata sabuwar waya ga kudi daya ke kashe mata.
Mal Yakubu ya sanar da uwale zaije gida ya sanar da kawunsa da nata yan uwan za'a zo neman auren Hanan dana Dije. Uwale da Sabuwa sam basu damu ba da jin Dije ta sami miji tunda Mal Yakubu yace wannan abokin ginin nasa ne zai aureta. Shima yana sane yaki fada don gudun kada su toshewa yar tasa hanyar arziki. Ita uwale harda cewa kyan da dama ya gaji ubansa, tunda ita mace ce gara ta auri mai aiki irin na ubanta.
Tunaninsa bai wuce ina ma Munari tana nan. Ina ma zata ga auren yarsu. Babu ranar da baya tuna su ita da Sadi. Amma gashi Inna uwale ta gargade shi ko sau daya yabi hanyar gidan su munari bata yafe masa ba.
Haka yaje kauyensu ya sanar da yan uwansa zancen auren ya dawo a ranar.
FARAR HAIHUWA💰28
Ranar asabar layin gidansu Dije ya cika sosai da jama'a. Kamar anzo daurin aure. Cikin kudin da take tatsa a jikin samari Hanan ta bayar aka hada sha tara ta arziki na tarar baki. Uwale ma tayo gayya sosai azo a ga yadda ake farar haihuwa. Tabarmi aka shimfida a tsakar gidan dama ta fadawa Mal yakubu masu kawo kudi da lefen Dije suje gidan gwaggo don bata son a hada su da yan uwan Ashir. Kasan harkar arziki bata dadi data tsiya. Mal yakubu yace to. Ba musu ya sanar da Gwaggo ita kuwa abin yayi mata dadi.
Duka bayan laasar suka iso Zaliha tayi wa 'yan uwan sulaiman jagora gidan. Nan ta zauna dama ita bata taba wulakanta yayarta. Abin mamaki akwati takwas aka shigo dashi gidan gwaggo matan unguwa da wasu dangin mal yakubu na kauye suna ta mamaki. Sai ga wasu akwati uku inji uwar ango. Murna da guda har waje. Cikin dangin mal yakubu wata tace anya kayan Dijengala ne kuwa? Uwale tace aikin gini yake. Matan da suka kawo suka ce kayan Sulaiman Hassan ne da aka kawowa Dije. Ga kudin aure dubu dari sannan suna so ayi biki nan da sati uku. Gwaggo duk ta rude da murna. Ajiyarta ta dauko ta sami dubu ashirin da hudu. Haka ta dunkule musu a matsayin tukwici. Haka suka yi ta godiya aka tashi cikin farinciki. Kaya kuwa gwaggo ta rinka saka ido ita da zaliha saboda halin taro.
Can gidan Uwale kuwa akwati bakwai ne aka kawo. Hudu seti daban da wasu uku manya suma seti daban. Jikin Uwale sai bari yake taga kaya. Sai ta cangala kafa tayi nan ta kuma cangala kafa tayi can. Bakinta dana sabuwa sam yaki rufuwa. Suma sun kawo kudi har dubu dari biyu dukiyar aure sannan suna son ayi biki nan da wani satin kamar yadda Hanan da Ashir suka shirya. Uwale tace sun amince ya shiga daki ta dauko dubu hamsin da Hanan ta bata ta basu tukwici. A wulakance suka karba dama tun daga waje suke yada maganganu.
Bayan sun tafi Uwale da Sabuwa suka tafi gidan gwaggo kallon kaya. Sabuwa tace kada ace muna bakin ciki gara muje muga abinda aka kawo mata. Uwale tayi tsaki karshenta ma a ghana mazi go aka zuba kayan. Ba karamin kaduwa suka yi ba da suka ga akwatuna jibge a wurin. Uwale tace ko dai anyi batan kai ne wannan ne na hannan. Mata suka yi mata ca a ka. Na Dijengala ne..yarinya ba auren talaka ba. Sabuwa tace ai dijen ba daya bace a layin nan kila dai nasu ne. Gwaggo tace sai kiyi kuma Sabuwa. Kaya na yata ne Allah Ya bata. Bakin ciki karara a fuskarsu suka fita daga gidan. Sabuwa harda kuka wai mal ya haince su bai fada musu gaskiya ba. Uwale tace barni da dan banza ai wallahi Zaliha za a aura masa. Ni Yakubu zai cuta...
Gwaggo dai ta haye kaya ko tsinke taki bari a dauka kamar yadda suka yi da malam yakubu. Uwale sai aike take mata karshe ta leqo ta katanga tace zata hada ta da yan sanda. Tabarya gwaggo ta dauko ko ki sauka ko na rotsa miki. Tsohuwar banza.
Daren ranar kamar su sabuwa zasu cinye mal. Gwaggo ta ce masa munafuki ai da suka dauka mai gini me sai yayi musu bayani dalla dalla. Yanzu ya kira yaron ya fada masa Zaliha zai aura masa Dije tace bata so. Zaliha ta tashi cikin tsiwa tace wallahi nafi karfin auren dole. Mal Hafiz na islamiyarmu zan aura.
Uwale ta doke mata baki fakiri zaki dauko min zaliha kamar ubanki? Ba ubana ba dai sai dai....sabuwa tace karasa sai dai na wa? Mara mutumci. Ranar dai anyi tashin hankali a gidan har makota ana ji.
FARAR HAIHUWA💰27
Tun daga ranar da Sulaiman yaje gidansu Dijengala bai kara zuwa ba saboda yanayin aiki. Wata rana ya dawo a gajiye wanka kawai yake so yayi ya kwanta. Umma ta shigo dakinsa da sallamarta. Ya amsa yace umma yau kamar anyi min duka duk na gaji. Umma taca gashi kuma fita nake son muyi bayan sallar magriba ba. Ba damuwa indai kin yarda dreba ya tuka. Ya tafi tun dazu naga kaima kuma kai kadai ka dawo. Eh a hanyar gidansa nace ya sauka zan dawo da kaina. Tace to don Allah kayi hakuri idan anyi sallah mu je. Haba umma meye na rokona kawai dai ki shirya yau Ammar ne zai tuka.
Umma na zaune a baya tana kallon danta Sulaiman da yake kokarin yin ribas da mota sai Ammar da yake gaba shima yana cewa daddy nuna min birki sai na rinka danna maka. Dariya yayi yana ta biyewa yaron. Zuciyar Haj Bintu fes da jindadin yadda yake kula da marayan. Wani dan hawaye ya fito tayi saurin sharewa Allah Ya jikan Alhaji da Yusuf da sauran musulmi.
Kamar yadda ta fada masa gidansu Sakina suka nufa. Ammar yana ta murna ganin anyi parking a kofar gidansu mamanshi. Da gudu ya fita Sulaiman yace umma baki fada min abinda yasa zamu zo gidan nan a daren nan ba. Hmm wai yaron da zai auri sakina ne yace ya fasa. Dazu ta kirani tana kuka. Yaji tausayinta sosai suka shiga gidan tare. Yasan dai sunan mutumin Ashir dan wan babanta sun taba haduwa sau daya.
Umma ta jajantawa iyayen Sakina. Kishiyar mamanta tace ai Hajiya in fada miki wata shegiyar yarinya ya hadu da ita. Jiya da babansa yazo yake fada tun yanzu ta fara juya shi. shiyasa yace bai yadda ayi auren da sakina ba kada su wulakanta ta. Umma tace hakane kam. Yanzu ita zai aura kenan. Tace mata eh ranar asabar ma za'a kai kudi. Umma tace Allah Ya kyauta Ya kawo miki nagari. Shima Sulaiman ranar asabar din za'a kai kudin aurensa. Sai ku fadawa Alhaji don Allah.
Washegari Sulaiman yayi shiri officially zaije zance. Umma tasa sha a gaba tana ta dariya. Wato yau kananan kaya ka sa don kada ta sake yi maka wanka da kwata. Ai ni umma yarinyar nan sai addua...amma kazanta a jikinta ba kama hannun yaro.
Motar rannan ya gani a bakin layin. Yana karasowa ya ga Hanan zaune a gaba suna ta hira da saurayinta. Sai a lokacin ya tuna inda ya san shi. ASHIR! wanda zai auri sakina ne. Dama Hanan zai aura...lokaci guda hankalinsa ya tashi. Ita kuma irin halinta kenan yarinyar nan? Yayi godiya ga Allah da yasa sonta bai yi zurfi a zuciyarsa ba. Dama kyau ne ya rude shi wanda kullum umma ke masa nasiha akan baya dorewa.
A soron gidan ya ganta zaune akan tabarma can gefe kuma tumakin Sabuwa. Tuni ya dena jin kamshin turarensa sai warin wurin kawai. Kanta a rufe da wani hijab dakal dakal ya sunkuyar da kai. Yayi sallama tare da kiran sunanta da dan karfi...ta dago a firgice lah...dama kaine mijin da zai aureni? Yace baki amsa min sallama ba. Yi hakuri alekum salam. Tab sallamar ma bata iya amsawa ba. Ta ce ai baba yace inyi maka ladabi da biyayya kada ka fasa auren. Dije kenan ita ba ruwanta komai fada take baki ba linzami. Yana murmushi daga tsaye don bazai iya zama a wurin ba. Miko masa ruwa a jug din roba har zai karba tace a rijiyar gwaggo na debo ruwan dadi ne. Hannunsa ya mayar aljihu barshi kawai nagode kada nasha cholera. Ehhh me kace? Ba komai. Ganin ya rasa hirar da zai mata yace dama size din takalmi zaki bani da bra saboda hada lefe. Ta fito da idanu...bra? Wai breziya rigar nono. Ya gyada kai. Tabdi ashe ma kai dan iska ne. Ta mike tsaye gwaggo ta fada mana idan dan iska ya tare mu muyi masa waazi. Idan mugu ne muyi ihu. To kaga Allah Yana da wuta gidan yan iska da aljanna gidan mutanen kirki. Kuma zan hada ka da mal na islamiyya ma yace bulala ake yi. Dariya yake sosai idonsa harda hawaye lallai zamansa da Dije sai ya shirya. Ganin yana dariya ta fice daga gidan a guje. Shima tafiya yayi kafin ta tara masa jama'a.
FARAR HAIHUWA💰29
Itama Zulai da ta iso kanon washegari fafur tace bata yadda Dije ta auri mai kudi ba sai dai a bawa jikarta. Mal yakubu duk rashin son tashin hankalinsa cewa yayi idan danki ne sai ki bashi wadda kike so. Ta kuwa soma kukan gulma ita anyi mata rashin kunya. Duk gidan ba dadi. Hanan kanta sai da ta ciji yatsa sai dai bata damu sosai ba saboda Ashir ma yana da kudin sannan ta fara sonsa. Duk abinda suke don basu ma san harda sarkokin gwal gudu biyu da awarwaro bane wanda gwaggo ta dauke ana soma bude akwati. Tsoro taji kada uwale tasa ido a kai.
Duka kayan lefen ta nuna masa ya gani ya yaba ciki tace wannan babban akwatin shine na iyaye. Ya duba kaya ne masu kyau na maza da mata. Rabawa yayi har abokinsa modibbo ya samu shadda har biyu. Ya dauki manyan atampa har uku, shadda daya da leshi ya bawa gwaggo. Sannan cikin kudin wanda an fada masa ita ta biya tukwici ya bata dubu arbain. Wayyo gwaggo sai kukan dadi cewa take yakubu ayi haka? Duk ni kadai? Yace ki dai yi shiru kawai gwaggo ya sami yaro ya biyoshi gida da akwatin.
Uwale so tayi duk kayan a bata wai a raba tsakanin 'yan uwa. Mal yakubu yaki, akwatin daya kai kuwa ko tsinki bata bashi ba ya dauke kai abinsa. Duk wanda ta bawa sai tace na lefen Hannan ne. Na Hanan din dakinsu ta ajiye harda kudin ta hana kowa tabawa.
Ana ta shirye shiryen biki Hanan an tare gidan gyaran jiki. Dama dai duk iskancinta bata yarda maza su bata ta ba sai dai ayi abinda ba'a rasa. Jikin nan nata ya kara kyau sosai duk inda ta gifta sai kamshi. da kyar Mal Yakubu ya samu aka daidaita ayi bikin nasu duka sati biyu bayan an kawo lefen. Zulai ita ke kara haddasa fada a gidan a cewarta nema ake a cuci jikokinta. Sam bata zancen sauran 'ya'yan sabuwa da suke wajen babansu. Ita Sabuwan ce take musu aike idan ta dan samu. Macen tayi aure namijin kuwa ya zama dan daban kauye.
Ita dai Dijengala tamkar ba amarya ba. Aiki ake tula sosai da dakon kaya idan anje kasuwa. Duka mazajen dai sun yiwa mal yakubu adalci ance kada yayi musu kayan daki. Gwaggo ce kadai ta damu da rashin gyaran Dijengala. To ga rashin wayewa shiyasa babu abinda take iya yi mata sai dai sabulu da ta bata giv tace kullum tazo gidanta tayi wanka sau biyu safe da dare. Ga mai toni montana ta siyo mata. Dije idan tayi wankan sai ta laftawa jikinta mai har sheki take yi.
FARAR HAIHUWA💰30
Saura kwana hudu a fara biki mal Yakubu har yasa anyiwa gidan fenti sai Ashir ya sa Hanan ta fada musu ya saya musu gida a cikin unguwarsu amma layi daban. Uwale duk ta kidime kafin kace kwabo ta fara hada kaya. Jin haka zulai tace bazata koma kauye ba tunda gidan albarkacin jikarsu ne su biyu. Ba musu uwale ta aminci. Mal yakubu yace babu inda zashi tunda ba'a daura aure ba. Ya rage naka mai kashin tsiya shine abinda uwale ta fada masa. Sannan tace tunda Dije ma gidan masu kudi zata yi aure ita bata yarda a tafi da ita ba. Gara ku gana da ita sosai dama kafi sonta. Zaliha kuwa saboda irin cin mutumcin da su Uwale suka yiwa saurayinta har yace ya fasa auren itama kin binsu tayi.
A dan lokacin da ya rage kafin biki Sulaiman yazo ganin Dije har sau uku. A irin hirar da take masa ta shirme ya gane rabonta da mahaifiyarta tun ranar da aka sake ta. A ransa yana mamakin yadda mace saboda bacin rai zata iya yin fushi harda yarta. Ya kudiri niyar idan sunyi aure dole a nemi dangin mahaifiyarta.
Biki kam yayi biki amma tamkar na mutum daya akeyi. Dijengala kullum tana gidan gwaggo haka aka yi kamu da yini don Hanan bata yarda a hada su ba kuma uwale ta amince da hakan. Yadda take bin hanan sau da kafa yanzu ban jin tayiwa babarta irin wannan biyayyar. Mal yakubu dai yayi nasa kokarin da gwaggo. Burinsa kawai yaga an dauke Dije zuwa gidan miji ko ta samu sauyin rayuwa. Kamar yadda Umma ta bawa Sulaiman shawara tace ya kauda kai a lamarin bikin idan an kawo amarya sai yayi yadda yake so ttunda bata karkashin ikonsa. Dole ya hakura zuwa ranar daurin aure. Ita kuwa Hanan an kashe kudi anyi party anyi dinner ta kasaita.
Ranar asabar aka daura musu aure. Dijengala tasha kuka lokacin da aka zo daukarta zuwa gidan miji. Cikin kayan lefenta aka dinka mata wata atampa riga da zani. Rigar tayi mata burmemiya. Ga lalle da tayi hannu da kafa na salatif yasha gishirin kunshi yayi bakikkirin. Sai bakin lalle da aka zana mata wasu munanan filawoyi a hannu da kafa. Kana ganinta kaga wadda bata waye ba. Mayafi ta yafa kato fuska tasha jar hoda, an ja gira ta kara baki ga janbaki yaji bajau. Matan da suka zo daukarta dai dama an fada musu yar talakawa ce shiyasa basu damu ba. Indai Sulaiman ne sai ta gyaru ko taki ko taso. A bangaren Hanan kuwa kaya tasa na gani na fada tana taku daidai uwale da Zulai suka shige motar da zaa kaita a ciki.
FARAR HAIHUWA💰31
Gidan Haj Bintu cike yake da mutane yan bikin auta Sulaiman. Dama dakin umman a kasa yake sama ne wurin Sulaiman shiyasa jeren da yasa ayi mata dakin kusa da nashi aka yi. Gidan yasha gyara sosai ga kayan more rayuwa kala kala.
Su Gwaggo ne 'yan kawo amarya da wasu cikin dangin mal Yakubu. Gwaggo tayiwa Dije da ke kuka nasiha sosai akan zaman gidan miji. Wani dan maganin mata ta samu a wurin kanwarta ta bawa Dijen tuna gida ta fada mata ta rinka sha da madara amma bayan taci abinci. Ko a jikinta ta karba tare da godiya ta soke a gefen zaninta. Dama sulaiman ya roki gwaggo kada a dinke kayan lefenta idan an kawota zai bayar a dinka da kansa.
Da Bismillah Dije ta shiga gidanta. Wurin Umma aka wuce da ita tayi mata nasiha. Umma har tafara magana a hankali gwaggo tace ai bazata ji ki ba sai kin daga murya. Umma tayi yadda aka umarceta tace ki kwantar da hankalinki 'yata ni babarki ce. Dije ta daga mayafin da dama a dole ta rufe fuska kada gwaggo tayi fada tace da gaske? Ta juya wurin Gwaggo kinji ashe a nan din ma zan sami Mama. Umma tace har kin samu ma. Ta share idanunta to na dena kuka indai zaki rinka bari naje wurin babana da zaliha da Gwaggo. Gwaggo dai kamar ta doke mata baki. Umma da yan uwanta sai abin ya basu dariya. Ita dai burinta ya cika sulaiman yayi aure. Ya auri wadda da yardar Allah zata rike Ammar da gaskiya.
Lokacin tafiyarsu Gwaggo da kyar aka rabasu da Dije. Suka zama abin tausayi kowa cikinsu sai kuka. Zaliha bata sami zuwa ba saboda tasha zagi wurin sabuwa akan zama da tayi wurin Dije.
Jama'a na watsewa Umma ta shiga daki. Bayan tayi wanka mai aikinta ta kawo mata tea wanda ya zama kaidar ta duk dare ta dauki wayarta ta buga. Taso kwarai ace matar ta halarci bikin Sulaiman da sukayi a gidansu amma tana Saudia taje Umra. Shekararsu biyar da haduwa a makkah suka shaku duk da cewa Umma ta girmeta. Ba kowa bace matar face shugabar Muslimah Institute. Makaranta ce wadda take da bari daban daban na kula da lamuran mata musulmai. Ana koyar da ilimin addini,boko ga wadanda basuyi ba, girki, gyaran jiki da gida da sauran al'amuran zamantakewa na mata.
Bayan ringing biyu aka dauka da sanyin murya aka yi sallama. Umma ta amsa tace anyi bikin auta ba kya nan Malama. Kinsan cewa kinci bashi ko. Daga daya barin aka yi dariya kiyi hakuri Haj Bintu zan saka ango da amarya a addua. Umma tace to nagode malama amma akwai matsala wadda nake bukatar taimakonki wurin shawo kanta. Nan ta zayyana mata irin rashin gyara da Dije ta tashi dashi. Yarinyar tana bukatar a gyarata sosai kinsan halin mazan yanzu. Sannan harkar ilimi duk da tana da matsalar kunne dole ta sami abinda zata samu a ilimin addini. Malama ta ce hakane Haj ai kinyi jihadi da kika bashi shawarar aurenta. Da ana samun iyayen miji irinki da mata sunji dadi sosai. Allah Ya biyaki da mafificin lada. Ki kaita makarantar ko zuwa next week ne kafin na dawo. Zan zauna seminar ne da za'ayi sati biyu masu zuwa. Ke dai in kika je saudia dama sai munyi cigiya kawai. Allah Ya dawo daku lafiya. Amin malama ta amsa sannan ta ajiye wayar.
Shiru tayi tana ta tunani har taji an taba mata kafada. Maama tunanin me kike yi ne haka...ta kalli dan da ya rage mata a duniya tayi murmushin bakinciki. Tunanin Khadija nake. Allah kadai Ya sani ko tana raye. A gabanta ya durkusa Maama kiyi hakuri da yardar Allah zamu gano inda Baba ya tafi da ita. Ta gyara glass din idanunta tare da mikewa tsaye. Allah Ya amsa adduarka Sadi.
FARAR HAIHUWA💰32
Wani katon gida aka kai Hanan a kundila. Tun daga bakin gate Uwale ta saki baki tana kallo. Suna shiga gidan ta kare masa kallo sai kuka...wai ni Uwale ce a cikin irin wannan gidan a matsayin gidan jikata. Ta kama hannun Zulai kam suka hau bene tare. Komai na gidan yayi kyau har da amaryar da aka kawo. Zulai tace Uwale yau kinga farar haihuwa ko. Na gani Zulai na gani. Allah Ya saka miki da alkhairi da kika bani Sabuwa. Wallahi taci karenta babu babbaka har abada bazan taba bari dan nan yayi mata kishiya ba. Haka mata suka yi ta kallo ana son barka.
Bayan sun tafi ya rage saura Hanan da kawayenta uku. Hajara ta jawo ta gefe sauran suna gyara inda aka bata to kinga dare ya fara yi ki tashi ki sake yin wanka. Hanan ta tashi zata shiga toilet...Hajara ta miko mata wani ruwa baki a leda, Babba ne yace kiyi wanka dashi kada ki goge jiki kawai ki bari ya bushe sai ki shafa mai. Wata shewa Hanan tayi shegiya Hajara yar gari ashe baki manta ba. Nagode yar uwa. Haba ba komai, idan kika yi amfani dashi ko kaska albarka don like miki zaiyi. Nima tun last week nayi ai kuwa na kama Alhaji a hannu. Hanan tayi dariya ranar aurenki zaki yi bayani idan miji yaji fayau. Ni kinga hankalina a kwance yau. Baki san akwai kayan mayarda mace budurwa ba? Au ke kin yarda Hajara to wallahi duk bige ne, once aka bude hanyar nan an bude kenan sai dai 'yan dabaru wanda basa hana mai hankali ganewa.
Ko da tayi wanka wata rigar bacci ta saka shara shara mai santsi. Dogon gashinta yasha gyara ta taje shi baya. Jikinta da kayanta sun sha turare kala kala. Samun wuri tayi ta kashingida akan gado sanyin AC na kada ta tana jin waka a hankali a waya. Ashir shi kadai ya shigo da leda a hannunsa ya rufe kofar dakin. Cikin sigar yanga da daukar hankali ta tare shi. Kallonta yake cike da shaawa har ta ajiye kayan da ya shigo dasu a kan kafet. Hankalinsa duk ya tashi da kyar ya iya hakuri suka ci kaza da dan juice. Ta sake tashi cikin yanga tana karkada jikinta. Ashir kamar wani mahaukaci ya fizgo ta ta fado jikinsa. Yana taba ta shaawarta ta karu a ransa. Kan gadon ya kwantar da ita tana murmushi....abinda ya faru bayan nan shine ya mugun daga mata hankali. Ashir baiyi wata wata ba daga kwanciyarta ya juyata akan cikinta ya danneta. Tun tana dariya ta dauka wasa yake har ta soma kuka. Gashi saboda karfin maganin data yi amfani dashi sau hudu ya nemeta a daren ta bayanta. Duk yaji mata ciwo...yasha zagi da Allah Ya isa tafi a kirga. Shi kuwa ko a jikinsa...Ashir rikakken homosexual ne bata sani ba. Da wannan dabiar yayi kudi lokaci guda.
Gabanin asuba bacci ya soma daukarta. Yana yin juyi ta share hawaye da sauri zata gudu. A kofar toilet ya tare ta ya sake danneta. Wannan karon ihun ma ta kasa yi saboda muryarta har ta dashe, sai nishi kawai take da kyar.
Dije tana ganin babu kowa a dakin ta bude fuskarta ta karewa dakin kallo. Tashi tayi tsam ta leka nan ta leka can. Komai yayi kyau tace uhm kaga gidan 'yan gayu. Sanyin AC ne ya fara damunta gashi bata san daga ina yake fitowa ba bare ta kashe. Ta karasa yaban wani karamin fridge ta bude. Lemuka ne da ruwa a ciki duk sunyi sanyi. Ta zauna bakin fridge din ta bude daya tana sha har gaban rigarta na jikewa.
Sulaiman tunda ya shigo gidan wani nishadi yake ji. Yayi murmushi yau kuma bai san shirmen da Dije zata yi masa ba, a hankali ya bude kofar dakin a tunaninsa tayi bacci don sha daya saura na dare. Zaune ya ganta gaban fridge tana shan juice. Ya kulle kofar ya karaso ciki. Inuwarsa kawai ta gani a kanta ai kuwa sai ta zabura ta tashi zata gudu. Hannunta ya kama ya janyo ta...wani irin abu yaji ga dai kamshi tunda Gwaggo ta sa mata humra ga wani wari wari da bai gane masa ba. Ta kwalo ido shikenan ka kamani amma wallahi ba sata nake ba. Umman nan gidan ce ta ce min wai komai na dakin nan nawa ne. Kuma dai babu wanda ya bani abinci tunda nazo. Rabona da abinci fa tun dumamen safe. Zaunar da ita yayi ya ajiye plate ya zuba nama da yoghurt a gabanta ga abinci kici. Da murnarta ta dauki cinyar kaza sai kuma tayi saurin mayarwa....ta daga gira daya na gano wayonka. Ai indo da tayi aure ta fada min wai idan miji ya kawo kaza ba'a ci idan ba haka ba ranar....ya girgiza kai ranar me? Ni ba ruwana amma dai bazan ci ba. Yayi yayi amma taki ci sai yoghurt din tasha. Tana zaune a gefe yaci ya koshi ya tashi yin wanka. Kafin ya fito tayi bacci. Kan gadon ya dora ta a hankali...wai yadda take wannan tashin bazai iya kwanciya kusa da ita ba. Filo yasa a kasa da bargo ya kwanta. Can cikin dare wuraren karfe uku yunwa ta tasheta da sanda ta duba taga yana bacci. Sauran naman ta dauka tana ci da sauri tana kora ruwa idanunta duk a kansa. Buruntun ta ya tashe shi amma tunda yaga abinda take yi ya share don kada yayi motsi ta kwana da yunwa. Ga dariya na cinsa dole ya gimtse. Ita kuwa tana gamawa ta koma gado ta kwanta sai bacci.
FARAR HAIHUWA💰33
Washegari amaren kowacce ta tashi da sabuwar rayuwa. Hanan bata sami yin bacci ba sai da gari ya gama wayewa. Da kyar ta iya tashi Ashir ne ya taimaka mata kamar babu abinda ya faru. Ruwan da ta shiga kamar an saka barkono don zafi amma haka ta daure saboda ta sami saukin ciwon. A wani irin yanayi tayi sallah don zama ya gagareta. Haka dai ta lallaba tayi sannan bacci ya dauketa. Sai wuraren shadaya na safe taji ana shafa mata fuska. A gigice ta tashi ta soma kuka. Ashir ya jawota yana rarrashi...haba amarya ai duk matar aure ranar da aka kaita sai tayi hakuri. Ni ban taba samun nutsuwa da mace kamar ki ba, nagode sosai. Ita dai a tsorace take kallonsa. Ya dauko mukulli a hannunsa yana murmushi..ga gift dinki for being a good wife. Duk abinda kike so sai kiyi magana. Ita tsoronsa ma take ji yanzu wace magana zatayi. Kamar ya karanci abinda take sakawa a ranta yace kinga sauran auren dana yi ban iya gabatar musu da bukata ta ba saboda basu waye ba kamar ki. Yanzu tunda jiya anyi yadda nake so yau kuma irin naki za'ayi kinga an jefi tsuntsu biyu da dutse daya kenan. Yana magana yana kashe mata ido. Ai tuni jikinta ya fara bari sai hawaye. Ashir kayi hakuri don Allah jikina ciwo yake min sosai. Allah Sarki Hanan nima haka fa..na rasa abinda yasa na kasa hakuri dake. Bari ayi wannan sai inyi miki tausa ko. Bai kara saurarta ba sai kukanta kawai ake ji. ko ta ina jini kawai take zubarwa saboda karfi yake saka mata.
Tunda Sulaiman ya dawo daga masallaci yake kallon Dije. Ita kadai akan gado amma duk bedsheet ya tattare. Ta juya nan ta juya can. Zama yayi akan gadon kusa da ita yana kallon fuskarta. Zanen kalangun da uwale tasa ayi mata ranar sunanta ya gani. Hannu ya kai ya taba ta yi saurin tashi da ihu. Tana ganinsa a zaune tace gizo gizo a fuskata. Ya girgiza kai, khadija da sunan Allah ake tashi ba ihu ba. To amma ai ji nayi ana bin fuskata. To yi hakuri zane na gani a gefen fuskarki. Hannu tasa ta rufe, ai Inna ce taso ta cuce ni wai sai anyi min kalangu irin nata. Mama na kafin a saketa tace bata yarda da shine aka fasa. Allah Ya saka mata da alkhairi da ta hana. Kinsan zanen jiki babu kyau.
Yanzu ki tashi kiyi wanka kiyi sallah, zan ajiye miki kaya. Anjima sai muje akai miki dinki ko. Ba musu ta mike. Bata fi minti biyar da shiga ba ta fito saman fuskarta duk kumfa. Ta sako katon hijab. Lokacin karatu yake amma idanunsa na kanta. Yana kaiwa aya yace koma Khadija wannan wankan ai na tada dauda ne. Baki ta turo masa ni a gida ma ban saba dadewa irin haka ba. Ruwan ne naga yayi min yawa. Ajiye Quran din yayi ya dan sha kunu wuce muje ki sake wanka. Wai a gabanka kake nufi. Ya gyada mata kai. To Al'Quran bazani ba. Tabdi kamar wata yar....toshe mata baki yayi kafin ta karasa zagin ya kinkime ta sai toilet. Wallahi wani karni kike yi ya fada a hankali.
FARAR HAIHUWA💰34
Allah Yasa akwai falo kafin dakin nasu amma duk da haka yadda take ihu yasan kila umma ta ji kukan. Duk da yadda take ihun ya bashi dariya yau daurewa yayi yace ta cire zanin da hijab. Kuka ta saka masa tana ta surutai. Bai kula ta ba ya cire jallabiyarsa ya rufe kofar.
Ta riga shi fita daga toilet din sai harararsa take kamar idonta zai fado. Shareta yayi ya dauko mai me kamshi ya shafa mata. Dole Dije tayi karni ga gashi bata askewa watarana ma wankan ba sabulu ga baki baya samun gyara sosai. Komai sai da ya gyara mata. Dama sunyi magana da umma akan Muslimah Institute sai dai baya so taje a muguwar kazanta shiyasa yake son ya dan gyara mata jiki. Kayan da ya dauko mata pakistan ne riga da wando da karamin mayafi, sai da duk suka sha turare itama ya fesa mata na jiki yace tayi sallah. Bayan ya gama da ita ya shiga yin wanka. Duk sanda suka hada ido sai yaga tana harararsa ko ta murguda baki. Kyayi kya gama mai tsiwa kawai. Ga kurma da son zance tace banji ba me kace? Cewa nayi muje a sake wanka...dakin ta bari gabadaya harda bugu masa kofa. Sai a lokacin yayi dariya...sannan yaji son matarsa yana shigarsa.
Dakin umma ya tarar da ita tana bata labarin yadda yayi mata wanka...wallahi umma duk ya gurje min jiki da soso.Umma ta sunkuyar da kai kasa ita ce mai jin kunyar. Ni ki barni na rinka kwana dake kawai shi Sulaiman din nan...kul ki dena kiransa Sulaiman mijinki ne kinji khadija. Tace to Malam haka mama take kiran babanmu. Shi dai saboda kunya fasa shiga dakin yayi.
Inna da Zulai tunda aka kai Hanan yau kwana hudu basu da zance sai na gidanta. Ba don Sabuwa ta dage kada suje gidan su zubarwa 'yarta da mutumci ba da tuni washegari sun je. Jira suke ta cika sati biyu kamar yadda Sabuwan tace sannan suje.
Shi kuwa Ashir soyayya sabuwa yake nunawa matarsa sosai. Kullum yana manne da ita. Kuka tayi har ta gaji ga wani masifaffen tsoronsa da take ji yanzu. Tun ranar da aka kaita ya karbe wayarta a cewarsa honeymoon suke a gida shiyasa ta kasa kiran Hajara ta tura ta gidan Babba gara a warware asirin da irin wannan rayuwa gara ta mutu ba aure. Itama Hajaran tafiya ta kama ta shiyasa bata zo ba. Duk bakin da akeyi a gabansu yake zama don yayi mata warning idan ta kuskura ta tona masa asiri zata ga abinda zai mata. Duk dare sai tayi kuka.
FARAR HAIHUWA💰35
Sati daya da bikinsu Hanan sannan Zaliha taje gidan. Mai aikin Hanan ita ta kaita har falo tace bari na kira antin. Tun da Hanan ta bullo Zaliha ke yi mata wani irin kallo. Wata irin tafiya take yi a tattale kamar sabuwar yar kaciya. Duk ta fada ma...zaliha taji tausayinta ta tashi da sauri ta rikota. Yaya sannu baki da lafiya ne? Wani hawaye ne yake kokarin saukowa Hanan wanda Zaliha ta lura dashi. Muryar Ashir ita ta sa Hanan saurin shanye kukanta. Daga wani falo suka fito da abokinsa wani dan saurayi wanda Ashir din ya girme shi. Babban Yaya ina wuni. Cikin faraa ya amsa mata. Ya sami wuri ya zauna kusa da Hanan. Tana son yin hira da 'yar uwarta yayi kane kane a wurin. Dole suka rinka hira suna sawa dashi. Yace Hanan bazaki nunawa Zaliha motarki ba? Yaya har mota gareki bamu sani ba. Hanan tace ai zanzo da ita gida ku gani. Amma sai tayi wata daya Ashir ya fada tare da mikewa. Muje kiga motar sai na kaiki gida. Kamar tayi kuka Hanan tace haba daga zuwanta ko ruwa bata sha ba. Kallon da yayi mata yasa tayi shiru, ita kanta Zalihan sai da tasha jinin jikinta ko akwai matsala. Daga wurin motar kuwa cewa yayi ta biyo shi gareji su tafi. Dole suka yi sallama ta tafi. Suna fita waje tace gidan daya yayar tawa zani a bompai fa. Da ka ajiyeni ma kawai. Wani kida yake ji a hankali ya kalleta. Maimakon ki nemi miji kiyi aure sai ki zauna tsurku gidan yayyanki. Maganar ta kona mata rai ta sha kunu. Sauke ni a nan...kamar bai ji ba ya kara taka mota. Sai da ta tsorata. A bajin junction kafin a bada hannu yace ta sauka tare da mika mata naira dari ta shiga mota. Bata iya masa godiya ba ma tayi saurin yin gaba.
A gidan Dije kuwa a falo ta gansu ita da Ammar suna shan mangwaro duk sun bata jikinsu. Dije na ganinta ta tashi da gudu suka rungume juna. Zaliha tayi murnar ganin yadda yayar tata ta fara yin fes. Tace Dijengala ta maigari. Ammar ya tashi sai na fadawa Daddy na kin ce ma mommy dijengala, yace sunanta mommy amma shi da umma khadija suke kiranta. Zaliha tace tohh yi hakuri kaji mommy nake nufi. Ya koma ya zauna to zo ki sha mangwaro. Murmushi tayi ta zauna suna hira da Dije. Muje ki gaisa da Umma tana da kirki sosai tace ma zamu zo mu gaishe da su Baba. Ta washe baki, in fada miki Daddy din Ammar yace zai siya min waya mai touch me touch you. Zaliha sai dariya suka je ta gaishe da umma. Umma tayi murna sosai tace mata ya mutan gida ina Gwaggo. Duk suna nan kalau. Hira suka yi sosai da Dije inda zalihan ta bata shawara akan ta rinka nutsuwa ta kuma rinka yin tsafta.
Sai bayan magriba ta shirya tafiya bayan taci abinci ta koshi. Umma ta hada mata kayayyakin yan mata. Sulaiman ya hadu dasu a bakin gate Dije taje rakata. Fita yayi daga motar yace drebansa ya kaita gida. Shima dubu goma ya bata tana ta godiya. Sai da Dije tayi kuka tana cewa ki gaishe da Baba da Gwaggo, da su Inna duka.
Har daki ta same shi duk da bata son zuwa kullum sai yasa tayi wanka sau uku kwamar wata kwaduwa. gashi na safen shi yake mata . Sai ta yini tana murguda masa baki. Kamar yadda yake koya mata da sallama ta shigo. Ya daga kai ya kalli gaban rigarta. Khadija me ya sami kayanki haka? Wallahi mangwaro ne amma kayi hakuri zanyi wanka yanzu, tasan karshen magana yace shi zai mata ne. Kin fiye tsoro ai babu abinda zan miki. Ta durkusa a gabansa Daddy din Ammar nagode sosai Allah Ya saka da alkhairi ya kara budi. Cikin rashin fahimta yace me ya faru. Kudi da yawa ka bawa zaliha shine nace nagode. Khadija kanwarki ai kanwata ce kinji ko. Tace to...amma dai ana son godiya. Kamar yanzu idan nayi wanka sau ukun nan yakamata ka rinka gode min. Hannunta ya janyo...nagane wato dai kina son na rinka yaba miki ko. To jeki kiyi ki fito kina kamshi kuma. Da sauri ta tashi ta shije toilet din.
Fafur Uwale da Zulai suka ki yarda a gidan Dije aka bawa zaliha kudi da kayan data zo dasu. Zulai tace kina nufin naira dari kawai aka baki tace eh mana. Ni mijin nata wallahi kamar bashi da kirki. Ahir na sake jin haka inji uwale kema ai kinyi garajen zuwa ne. Kuma ba gashi kince ya siya mata mota ba. Ai kina ganin ashiru kinga arziki. Shima mijin Dijengala nasan duk na neman suna ne ko yanzu ya lura kin fita kyau yana son yin canji. Zaliha tace da wa???Allah Ya kiyaye na auri wanda ya saki yayata.
FARAR HAIHUWA💰36
Cikin dare Uwale ta rinka juyi sam ta kasa bacci. Duk da taki yarda da abinda Zaliha ta fada masu lokacin da ta je gidan yayyenta, ta kasa samun nutsuwa. Ya zama dole taje ta ganewa idanunta tun auren baije koina ba. Yaushe zata yarda wani namiji ya wulakanta Hannan da ranta da lafiyarta. Yarinya fara ga kyau ga kyan diri. Dole taje gidan gobe ta ganewa idonta don irin yadda take son Hanan ko da iyayen Hanan din ne zasu saba idan aka bata mata rai. Da wannan shawarar bacci ya dauketa.
Gari na wayewa ko zulai bata sanarwa ba ta fice daga gidan. Duk wanda mal Yakubu ya tambaya ina Innarsa sai su ce suma basu tashi sun ganta a gidan ba.
Bugu take ji a bakin gate kamar za'a balla shi. Da kyar ta iya ture Ashir ta tashi. Jikinta yauma ciwon yake ga wani zazzabi da take yawan yi da ciwon kai saboda kukan da take kwana tana yi. Karfe takwas ta gani da kwata, tsoronta daya kada ya sake tashi don idan idonsa biyu bata da hutu. Da sanda ta fita daga dakin ta sauka kasa. Mai aikinta Nancy ta gani tana jera abinci akan dinning table. Nancy jeki ta tambayi mai gadi waye yake bugu da safen nan. Ba jimawa ta dawo tace sunanta Inna Uwale, gurguwace. A harzuke Hanan tace gurguwar uwarki. Kice ya bude mata kakata ce. Duk duniya bata da masoyi kamar uwale shiyasa duk neman kudinta a wurin samari don ta kyautatawa kakar ne. Uwale na shigowa ta tsaya turus, komai na gidan yayi ga kamshi yana tashi sai dai Hanan ta fige kamar kazar mayu. Auren sati daya duk idanunta sunyi loko. Ba dole ba tana tare da fargaba. Hannan me ya sameki? Tuni hawaye ya cika idonta sai dai kafin tayi magana suka ji muryar Ashir yana saukowa daga bakin benen. Sweety ke da baki da lafiya me ya taso ki yanzu zo muje nayi miki tausa. Zuciyar Hanan ta tsinke da jin muryarsa. Ita kuwa uwale duk kunya ta kamata. Shima sai yayi pretending kamar lokacin ya ganta harda sunkuyar da kai...au Inna kece da safen nan? Hanan ya kika barta a tsaye ku zauna mana. Kusa da Hanan din ya zauna don kada ta sami damar magana. Uwale ta durkusa har kasa ta gaishe shi haba Inna ai sai kisa naji kunya ya fada yana kallon Hanan. Kwana biyu zazzabi take yi shiyasa kika ga duk ta fada. Rashin hutu ke damunta saboda baki. Hanan tayi saurin kallonsa...ji karya banda Zaliha ko yan gidansu babu wanda yazo. Tafiya zanyi da ita America ta huta na wata daya kafin su koma makaranta. Uwale sai murna Allah Sarki Ashiru Allah Ya baku zaman lafiya. kana ta dawainiya mungode sosai. Haka suka yi ta hira Uwale har ta fara hadiyar yawu saboda yunwa. Ga abinci kala kala tana hangowa amma masu gidan basu yi mata tayi ba. Ta dan kiftawa Hanan ido zo ki nuna min bayangida zan dan zaga. Ashir yace bari Nancy ta kaiki. Tana shiga toilet din tayi tsaki dama niyarta tace mata bazata bata abinci bane. Data fito a nan inda ta barsu ta samesu. Zata kuma zama Ashir yace Inna muje insa dreba ya kaiki gida ko. Hanan tashi kije kiyi wanka ina zuwa. A tsorace ta mike tace Inna ki gaida su Baba. Sai anjima. Mamaki karara a fuskar Uwale ta tashi a sanyaye don yadda ya hade fuska bata ga damar yin musu ba. Suna fita yace wa dreban ka ajiyeta a bus stop ta sami mota. Inna ki gaida mutan gida. Haka ta tafi ko na pure water bai bata ba. A zuciyarta babu abinda bata saka ba.
*
Kaga ni nayi kyau? Green din material ne a jikinta riga da skirt sai wani purple din hijab mai duhu data saka. Murmushi yayi sosai ma Khadija ta ce to daga yau zaka dena min wanka ko? Kullum sai nayi istigfari dari fa saboda nasan ba kyau. Fin karfina kawai kayi. A sati biyun da suka yi a matsayin mata da miji kullum akwai shirmen da Khadija zata yi masa. Don ma Umma tana tayashi yi mata gyara. Yanzu waya fada miki idan miji yayiwa mata wanka laifi ne? Oho ta bashi amsa. Ya dan zare mata ido tayi saurin cewa ina nufin ban sani ba. Haka na zata akwai zunubi. Yace to babu kinji ko. Yau zamu je asibiti a duba miki kunne sannan na kaiki makarantar kawar umma. Wata dariya tayi har kasa Umma tana ji tace ai asarar kudi zakayi idan ka kaini makarantar Inna Uwale tace bani da kokari, kuma fa gaskiya ne babu abinda na iya a makaranta sai Arais okon pashon. Sulaiman yayi dariya sosai yadda ta dage ta kai karshen national anthem. Tace to meye na dariya ko ban iya bane? Shi dai wannan da karfi akeyi a makarantarmu shiyasa na iya. Ya riko hannunta zasu fita daga dakin ....gaskiya kin iya sosai Khadija. Tace don ma mura ta dan kamani ne fa amma wata malamarmu tace ina da muryar waka. Idan na fara sai kaji ana ta tafi. Yana dariya yace don Allah kada kisa cikina ciwo. Shige mu tafi.
Asibitin suka fara zuwa likitan ya bata magunguna na sha da na digawa a kunne ya badu sati biyu sannan su dawo sai asan abinda za'ayi wa kunnen. Daga nan suka wuce Muslimah Institute. Office din Director din suka wuce wanda tun a bakin kofa aka rubuta sunanta.
HAJ MAIMUNATU ADAM
FARAR HAIHUWA💰37
Kwankwasa Sulaiman yayi tare da sallama. Daga ciki aka amsa ya bude suka shiga. Khadija ta kalli kan kujerar ta koma waje ta sake karanta sunan dake jikin kofar. Kaine Haj Maimunatu Adam din? Ta kalli Sulaiman, daddyn Ammar sunan mace nagani fa kaga namiji kuma yayi kwam akan kujerar. Salati Sulaiman yayi yace zaki fara ko.? Don Allah kayi hakuri ya fadawa matashin dake harhada wasu files dake gabansa. Matashin da zai kai shekaru ashirin da biyar ya tuntsire da dariya jin abinda Khadija ta fada. Mama na ce Haj Maimunatu din. Sulaiman ya mika mishi hannu suka gaisa. Kayi hakuri tana da matsalar kunne ne. Hajiyan bata nan ne? Eh ta fita Inno, sorry mamanta ce ta zame dazu shine ta tafi asibiti wurinta. Kaine Alh Sulaiman Hassan ko? Don ta fada min zaka zo da matarka. Sulaiman yace eh. To ga wannan form din ka cike. Maama tace zata shiga ajin karatun boko da islamiyya wanda akeyi sunday zuwa wednesday. Ranar alhamis da juma'a ba karatu. Sai kuma special class na mata shi kuma bayan an gama karatun safe ranar asabar da lahadi akeyi. Sulaiman ya karbi form din yana karantawa. Ajin matan ana koyar da girki da yadda mace zata gyara jikinta. Sannan ana yin gyaran jikin gaba daya har da gashi. Khadija sai bin bakinsu take da kallo don bata jin abinda ake fada sosai. Harda certificate ake bayarwa a makarantar. Sulaiman ya zabi ajin da yake so ta shiga sannan ya jaddada masa kurma ce amma tana ji kadan kadan. Sun yanke shawarar washegari zata fara karatu. Da zasu tafi Sulaiman ya ce ya sunan malamin ne? Sadisu Yakub. Amma ana kirana Sadi. Suka sake musabaha sannan suka tafi gida bayan sun karbi uniform din makarantar wanda dogon hijab ne har kasa ruwan kasa.
Sati hudu da fara karatun Khadija ya fara ganin changes. Kullum dare bata barinshi yayi bacci da wuri sai ya sake koya mata karatun da aka yi. Tace masa tana son yin ta daya idan anyi jarabawa...wallahi duk karatun da nayi ta karshe nake zuwa kamar na gaji dakikanci.
Ranar da ta fara ajin gyaran jiki relaxer aka saka mata a kanta saboda yadda yayi karfi sanan aka yi steaming. Ashe yana da dan tsaho ba laifi. Tun daga ranar take yanga da gashi. Tana jin dadin yadda kullum Sulaiman yake tabawa don kuwa Mal Amina ta sanar dasu ba'a boyewa miji jiki. Gyaran jikin da ake yi mata yasa fatarta ta yi kyau sosai. Jikinta kullum kamshi. Yau da yake an koya musu kwalliya irin ta zamani tana dawowa bayan taje sunyi girki da mai aiki wanka taje tayi ta zauna gaban mudubi gyaran fuska. Ita kanta tasan ta canja sosai. Sai da ta tabbatar tayi kyau sannan ta tashi ta hau shafa humra da fesa turaren jiki. Riga da skirt ta saka yan kanti ta saka ribbon a kanta. Tana gamawa ta dauki hearing aid dinta wanda likita ya bata a asibiti ta saka a kunnen hagu, kunnen daman bai tabu ba sosai .ta dauko wani wata zuma cikin kayan da mal Amina tace su rinka sha duk kwana uku kafin miji ya dawo.
Yau tayi niyar fada masa ya dena kwana a kasa. Tun safe take tunanin da yadda zata fada kada yace tayi rashin kunya.
A falo ya ganta suna kallon wani cartoon ita da Ammar. Da sallama ya shigo Ammar yaje ya taro shi. Mommy bazaki zo yiwa Daddy na oyoyo ba. Kai ta sunkuyar tace sannu da zuwa. Abin mamaki Dije kurma ta koma khadija yar gayu. Wai ita ce take jin kunyarsa yan kwanakin nan. Ya sake kallonta...tayi kyau kamar ba ita ba yace ina Umma ne. Yanzu ta shiga daki ta bashi amsa. Dakin ya bita suka dan taba hira sannan ya hau sama. Wani kamshi mai dadi ne ya ji a dakin ga kayan bacci ta ajiye masa akan gado. Dadi yaji sosai yana kara godewa Allah daya bashi ikon karbar shawarar mahaifiyarsa gashi yanzu ba karamin son khadija yake ba.
Dawowa kasa yayi yace a kashe film din haka sai gobe. Ammar tashi ka tafi daki ka kwanta. Ni daddy ba na jin bacci. Ka bari muyi hira da mommy. Tabdi ai shima Sulaiman hirar yake son yi da ita. Khadija kai min abincina daki bari na kai wannan dan naki da kike shagwabawa wurin kakarsa. Ba musu ta tashi...binta yayi da ido har ta bace.
Ko yaya ya dago kai sai yaga tana kallonsa. Ya ajiye cokalin hannunsa wai ni khadija so kike na kware ne? Tayi murmushi tare da jin kunya a'a. To zo ki bani a baki yau ina ciwon hannu. Harda rufe fuska don kunya ta tashi zata gudu. Ya janyota ta fada kansa. To karya ni ya fada yana ture plate din abincin...tace yi hakuri. Nifa gaskiya duk kin wani zama salihar karfi da yaji. Ina kika kai min Dijengala ne. Nayi missing dinta kinsan ita ta iya tarairayar miji. Murguda masa baki tayi zata tashi wato ma tsokana ta kake yi ko. Sai idanunta ya ciko da hawaye ta fara masa kukan shagwaba...ya na share hawayen yace ba tsokanarki nake yi ba Khadija, sonki nake yi. Wata kunya taji zata sunkuyar da kai ya rike habarta ina bakin tsiwar nan ya kamata ace mun gaisa dashi....kissing dinta yayi sannan yace tashi muyi sallah. Ai nayi ta fada kanta a kasa yau kam kunyar sulaiman tayi mata yawa. Kada kice malamarku bata fada miki ana yin sallah ba tsakanin mata da miji don neman albarka kafin....ita ma kafin ya karasa magana ta gudu..
*
Kwanansu Hanan uku da dawowa daga America. Taci wahala sosai a hannun Ashir ga zulumi shiyasa kullum take kara ramewa. Ya kaita gidan iyayenshi sun gaisa. Hajiyarsa tayi ta mita sai yau kaga damar kawo mana ta kitse don kada ta narke?ko a jikinsa sai hanan ke aikin bada hakuri. Gidan nata iyayen har ta gaji da magiya yaki kaita. Wata rana da safe ta tashi tana ta amai duk jikinta ba dadi. Rabonta da lafiya tun ranar da aka kawota gidan gashi yanzu watanta uku. Komai na jindadin rayuwa yana bata banda kwanciyar hankali. Ta fito daga toilet ta canja kaya sanan ta sauko kasa ta kira shi ya taimaka ya kaita asibiti. tana bude falonsa ta ganshi tare da wani yaro da baifi shekaru sha biyar ba. Yanayin data gansu ne yasa ta sume.
FARAR HAIHUWA💰38
Motsin da yaji a bakin kofar yasa shi saurin juyuwa a firgice. Ya dubi yaron dama baka saka key a kofar ba. Yaro ya ce to ba gidanka bane? Ya harzuka kai rashin kunya zaka yi min mara mutumci. Yaron ya kalle shi ido cikin ido aut dama akwai wata kunya ko mutumci tsakaninmu. Ya dauki kayansa ya saka sannan yayi hanyar kofa ya tsallake Hanan dake kwance bata san inda kanta yake ba. Ashir mamaki ya kamashi lallai wannan yaron indai baayi da gaske ba sai ya fi su shaidanci. Amma zai gamu dashi. Hanan ya je ya daga ya nufi mota da ita. Shi yanayinta bai dameshi ba kamar rashin kunyar yaron. Gashi har ya fara sonsa! Subhanallah.
Bayan dogon bincike likita ya tabbarwa da Ashir tana da ciki wata uku, sannan jininta ya hau sosai. Ashir yafi kowa sanin dalilin lalurar matarsa. Likitan yana fita yace to munafuka dama labe kike yi min ko? To kinga uwar da ake yi a dakin sai me. Tana hawaye tace don girman Allah Ashir ka sake ni. Da irin rayuwar gidanka gara na mutu na huta. Wa ya fada miki mutuwa hutu ce ga kowa? Ai hutu ce ga mai rabo kawai wanda bana jin kina cikinsu. Ko baki san duk irin text din da kuke exchanging da kawarki hajara na gani ba. Shiyasa na hanaki wayar. Kuma bukatarki ta muyi auren har abada ya tabbata ba. Ni dake Hanan mutu ka raba. Don yanzu na fara sonki.Kudi da jindadin rayuwa kuwa yanzu kika fara gani. Yana gama magana ya fice tare da banko kofar har sai da gabanta ya fadi. Wani kuka Hanan ta rinka yi mai sauti duk ta zama abin tausayi. Tayi nadamar auren Ashir, da bin malamai da ma irin rayuwarta ta son abin duniya. Yau gata cikin kudi da daula amma bata da kwanciyar ko kadan. Tashi tayi a hankali tana jan karfen da aka saka robar ruwan da ake kara mata ta bude kofa ta fice.
Atampa mai kyau ce a jikinta wadda ta rufe ta da babban mayafi mai kauri. Kafarta takalmi ne mara tudu sosai da safa ta rufen jan kunshin da tayi. Fuskarta babu wani ado amma kana ganinta kaga kyakkyawar mace. Farin glass din idonta ta cire zata goge ta hango Hanan tana tafiya a hankali tana bin bango. Da sauri ta karasa ta tareta don saura kadan ta fadi. Sannu baiwar Allah me ya fito dake haka babu wanda ya rike ki. Wani irin numfashi Hanan take yi tace don Allah ki taimakeni ki bani aron waya na kira babana. Ka ji wahala tasa ta tuna babanta yau!!!
Nuna min dakinki tukunna kinga jikinki babu kwari. Cikin kuka tace a'a ni dai ki kira min idan yazo ya ganni hanawa zaiyi. Dankwalin kanta ta cire ta shimfidawa Hanan ta zauna sannan ta dauko waya a jaka ta bata. Duk wanda ta kira bata samu cikin iyayenta. Gashi number dinsu kadai ta haddace. Ita Sabuwa dama wayarta kamar hoto bata fiye kula ta ba. Shi kuwa mal Yakubu ya canja waya batare da saninta ba. Sulaiman ya sama masa aiki a daya daga cikin kamfanin sa. Ta kara fashewa da kuka na shiga uku na lalace. Subhanallahi kina musulma me ya hadaki da wannan kalma. Ki yi hakuri komai yayi zafi maganinsa Allah. Ina kika bar azkar da addua, ina tawakkali da imaninki. Hanan ta rungume ta tana kuka na cuci kaina. A nan wurin cikin kuka da dashewar murya ta fada mata yadda ta auri Ashir da irin halayyarsa. Ya hanani hulda da kowa a gidanmu. Wayata ma tana hannunsa. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Kiyi hakuri mu koma daki sai ki bani kwatancen gidanku zani da kaina. Ai bai kamata mahaifinki yayi fushi dake akan hakan ba. Sai dai kinyi kuskure babba da kika rayuwarki da sabon Allah. Bin bokaye da malaman tsibbu hanyar shirka ce sai dai kuma Allah Yana duba zukatanmu a lokacin da muke neman gafararSa. Ki kyautata tubanki sai kiga Allah Ya kawo miki mafita.
Suna zuwa kofar dakin Ashir ya taho. Ganin Hanan a waje yasa yayi saurin karasowa yana muzurai. Sai yau ta tabbatar ashe mummuna ne...ko kuma munin halayyarsa ce yasa take ganinshi kamar wani kumurcin maciji. Ya wani kwantar da murya Sweety daga ina ke da nace miki ina zuwa. Me ya fitar dake. Ta kalli matar a tsorace alamun neman agaji. Allurar hannunta ke mata ciwo ta fito neman nurse. A hanya na ganta shine na rakota daki zan kira nurse din. Ya riko kafadarta no ba problem ki tafi kawai zan nemo su. Tana tsaye saroro ya rufo kofar. Kafin ta yafi taji yana yiwa Hanan fada. Gashi ko address din gidan nasu bata karba na. Dole ta koma dakin da Inno take kwance ta basu labarin abinda ta gani. Kowa ya tausaya mata.
FARAR HAIHUWA💰39
Saukar ruwan sanyi yaji a bayansa ya tashi da sauri. Dariya take yi sosai ganin yadda ya tsorata. Kanta ya yi tana gudu tana kiran Umma. Gara ma ki tsaya na rama kawai. Ai kin fini sanin sun tafi wurin Sakina ita da Ammar. Dama so kika yi su tafi ki takura min ko. Shiyasa kika wani langabe wai baki da lafiya. Ta tsaya tana haki washh...don Allah kada ka rama wallahi a magana jari na karanta labarin Yushau. Kuma ai kaine kace na rinka karantawa. Dana saki karatu ai ba cewa nayi ki gwada a kaina ba. Zama tayi tana mayarda numfashi da kyar. Tana yamutsa fuska. Gaskiya Daddyn Ammar na gaji daga sosai daga yin dan gudun nan. Gefen cikina har ya fara ciwo. sulaiman ya zauna kusa da ita. Zo mu gani Dijengala ina ne yake ciwon. Abinda yake mata yasa ta dariya... yace Khadija. Ta dan nutsu naam. Ina son kara aure...hawaye ya gani sharrrr yana saukowa ba kakkautawa. Meye na kuka kuma. Ta sake bari baki me nayi maka? Wankan nan yanzu sau uku nake yi a rana gashi ina maka girki da tsafta. Don Allah kace ka fasa. Yayi murmushi wai dama kina kishina? Sosai ta bashi amsa tana share hawaye. Na zata wanda ake so ake kishi. Ta zaro ido to ni an fada maka bana sonka ne? Kada ma ka yarda nema ake a hada mu kawai. Ta rike baki Ah...haka kawai ana so a saka min ciwon zuciya. Ni baki taba cewa kina sona ba shiyasa ma zan yi auren....rungumar sa tayi a cikin kunnensa tace I love you Sulaiman. Wani farinciki yaji sosai ya rike ta da kyau. To dama kishiyar taki mota ce ...ta dago kai da gaske? Sai murna take. Eh amma sai nan da wata biyu idan kin gama ajin mata naji ance kinfi kowa kokari. Daya ajin kuma sai naga kinyi da daya. Khadija tace zanyi mana ba dai kana min addua ba? Ina yi Khadija mommyn Ammar.
Tunda suka yi aure Mal Yakubu bai taba jin muryar Hanan ba. Kullum sai sunyi waya da Dije. Da farko fushi yayi saboda yadda hanan din take nuna bashi da mahimmanci a rayuwarta. Daga baya kuma yaga gara ya hakura ya cigaba da adduar shiriya gareta. Zaliha ya kira ya tambayeta ko Hanan ta canza layi ne don baya samunta a waya. Ta tabe baki Baba ai ta share kowa. Nima idan na kira bana samunta. Ya dauko dari biyar a aljihunsa. Gashi gobe kije gidan ki binciko min lafiyarta. Har ta mike yace wai yaushe rabon da kije gidan ma. Naje sau hudu amma sau daya na shiga. Idan naje kullum maigadi sai yace bata nan.
Jikin Hanan ya danyi sauki bayan tayi kwana hudu a asibitin sannan aka sallamota. Ta kara ramewa tayi baki sosai. Daren ranar data dawo Ashir yazo ya sameta a kwance. Kanta yayi ya danneta. Tana ta ihu Ashir kada ka danneni ka manta ina da ciki? Ya kara matseta kada ki damu bazan saka miki karfi ba nima ai ina son cikin. Kamar wata dabba haka ya juyata tana kuka da hawaye baiji tausayinta ba.
Washegari ta kasa tashi. Wani irin ruwa ne yake fito mata ta baya. Tun karfe takwas Ashir ya fita. Tana nan kwance mai aiki ta sanar da ita zuwan zaliha. Bude murya tayi tana kiran Zaliha iyakar karfinta.
Ko zama bata yi ba saboda wulakancin da Ashir yayi mata wancan zuwan. Yanzu ma a gate karya tayi tace ita yar uwar mai aikin gidan ce shiyasa ya barta ta shiga. Kwala mata kira taji Hanan tana yi. Da gudu ta hau saman ta ganta a kwance duk ta yankwane. Ta soma kuka yaya lafiya? Itama Hanan kukan take tace zaliha ki kirawo su Mama da Inna suzo su fitar dani daga gidan nan. Ashir zai kashe ni. Kiyi sauri kafin ya dawo.Bata jira karshen zancen ba ta sauka cikin sauri ko bas fada ba tasan Hanan tana neman taimako. Dole tayi sauri taje gida ta sanar da Baba. Kofar gidan taji a kulle gam. Ta juyu a tsorace tana neman mai aikin ta bude mata. Ashir ta gani da key a hannunsa ya hade rai sosai. Shegiya munafuka kinzo an fesa miki gulma ko.
FARAR HAIHUWA💰40
Mal Yakubu tun yana daukar abin da wasa har dare Zaliha bata dawo ba gashi baya samun wayarta. Gaba daya ya rude ya kira Dije ko tazo gidanta. Tace masa shekaranjiya tazo. Sabuwa yazo ya tambaya ko sunyi da ita zata kwana. Tace min ma bazata dade ba amma kasan halin yaran nan. Kila ta matsa mata ne akan sai ta kwanan. Zulai tace ni kana bani mamaki duk ka wani gigice. Ka bari gari ya waye munyi magana da Uwale zamuje gidan. Uwale dake sallah ta yi wani gyaran murya ehem ehem harda gyada kai wai ta gaskata abinda zulai tace. Inna kada dai ki bata sallarki ya fada yana zama akan kujera. Ku bari sabuwa zata je ai da girmanku bai kamata....zata yi ruku'u tace Assalamma alekum ta wani shafe goshi tare da mikewa, kaniyarka dan nan. Meye zaka ce bazamu ba. To ni da zulai zamu je idan sabuwan zata sai taje ni ban hana ba. Ni ba haka nake nufi ba Inna. Sai ku tafi gabadaya ba matsala. A wace unguwa gidan yake? Sabuwa tace ai dayake ba gidan 'yar so bane Dije kurma dole ka bari sai yau ka tambayi inda gidanta yake. Fuskarsa a hade ya dago kai Dije nine uwarta nine ubanta dole na damu. Kuma sau nawa tazo gidan nan, shima mijin yazo amma ita hanan ko akuya na bashi ai ya waiwayo ni. Uwale tace Hannan din ce akuya. Yakubu ka kiyayeni fa.
Yaro ne yayi sallama suka shigo su biyu da kaya niki niki. Buhun shinkafa ne, sukari, kwalin taliya da makaroni ga jarkokin mai. Uwale ta cangolo kafarta jikinta har rawa yake tace gasu nan ma yan halak. Dan nan tashi ka bawa Ashiru wurin zama. Mal yakubu ya kalli Inna duk ta kidime, ya girgiza kai. Muryar dattijuwa suka ji Zulai ta tashi kila uwar mijin ce Sabuwa samu ruwan sanyi. Umma ce ta shigo tare da Ammar sai Dije da Sulaiman a bayansu. Tsakin Uwale har waje don takaici. Zulai ta koma ta zauna dabas dama gata da kiba. Sabuwa ma dawowa tayi ta zauna. Cikinsu banda zaliha babu wanda ya taba zuwa gidan Khadijan Sulaiman. Da mal yakubu duk suka gaisa Umma tana ta gaishe dasu Uwale sukayi kamar basu ji ba. Dije ta durkusa har kasa ta gaishesu nan ma sai kaji ance uhm kawai. Ta kalli Sulaiman wanda ya gama hade rai kamar bai taba dariya ba. Yayi mata alamar ta tashi su tafi. Uwale tace kayan da aka shigo dasu bama bukata fa. umma tace haba Inna kawo muku nayi asa albarka. Uwale ta tashi tana cilla kafa aikin banza neman suna. King munyi kama da mayunwata ne? ta nuna Dije wannan bakar abar ita zaku bawa abinci uwarta ce tayi gadon tsiya. Mal Yakubu duk kunya ta kama shi don Allah Hajiya kuyi hakuri. Inna meye haka ne don girman Allah. Surukanki ne fa. Ahhh Allah Ya kiyaye waya sani ko barawo ne? Tun farko ai cewa akayi aikin gini dan naki yake yi sai daga baya kuma aka canza labari. Zulai tayi tsaki ai kece ma kike wani kulasu. Ayi dai mu gani...
Sulaiman ya gama harzuka ganin yadda matarsa take kuka saboda yadda su uwale ke yi musu rashin mutumci. Hannunta ya kama ya tayar da ita tsaye. Tashi mu tafi khadija. Uwale tayi wata shewa amma dai Allah Ya isa da ka kirata Khadija, kalle ni da kyau sunana ne, ga fari ga kyau . ainihin mai sunan ma balarabiya ce. Shine zaka kira wannan jikar barebarin. Mal Yakubu kamar yayi kuka yace Sulaiman dauki matarka ku tafi. Umma kanta boye fushinta tayi amma tasa a ranta akwai ranar da zata mayar musu da martani. Ita Sabuwa tunanin 'ya'yanta yasa basu isheta kallo ba. A mota Umma da Sulaiman suka yi ta bawa Khadija hakuri. Ace ranar da tazo gidan da uwar mijinta ranar ne Inna zata yi mata tijara irin wannan.
FARAR HAIHUWA💰41
Wannan daren da kyar Sulaiman ya samu kan Khadija. Tayi kuka sosai yayi ta bata hakuri. Can cikin dare tana bacci tana ajiyar zuciya ya kalli fuskarta da ta kumbura saboda kuka ya sake rungumeta. Wata tsanar su Uwale yake kara ji sannan ya yanke shawarar dole ya nemo mata mahaifiyarta idan kuma bata da rai ya nemo ko da mutum daya ne a danginta. Maganarsu da sakina maman Ammar ce ta dawo masa. Yaje gidansu bayan ya taso daga wurin aiki shine take sanar dashi irin wulakancin da Ashir yaje yayiwa Abubakar mutumin da yake neman aurenta yanzo. A yadda ta fada masa da sassafe yaje har gidansa yayi masa batacciya a cewarsa ai ba fasa aurenta yayi ba. Idan Hanan ta kwana biyu zai auro ta. Abin babu tsari sam...dawowarsa daga nan ne ya zo ya hadu da zaliha a gidansa. Dole ya samu lokaci yaje gidansa yayi masa warning...sakina ta wuce ya zuba ido ayi mata wulakanci irin wannan. Da wannan tunanin yayi bacci.
Su Hanan da Zaliha kuwa ranar sunga tashin hankali. Wayar zaliha ya karbe sanan yasa su a gaba da fada. Da rana nancy mai aikin gidan tayi abinci mai rai da lafiya aka kaiwa Hanan. Zaliha kuma garin kwaki da gyada aka bata. Ashir yasa su a gaba yace kowa sai yaci nasa kada su mace masa a gida. Ke zaliha kiyi hakuri kinji ko..dokar gidana ce babu wanda zaici dadi ya tada kai dashi sai iyalina. Suna kuka suna cin abincin. Hanan tana gamawa sai amai ya dubi zaliha to uwar gulma tashi ki guara wurin ai 'yar uwarki ce ta yi.
Alamun da ya gani cewa hanan na bacci shi ya bashi damar yin waya taji yana cewa an samu kanwarta ranka ya dade. Ba dai cewa kayi a sami wani daga cikin yan uwanta da take so ba wadda bata da miji. Ina ganin jinin wannan yarinyar ma zai yi, gobe sai azo a dauke ta. Ya dan yi shiru ba damuwa ai babu wanda zai zarge mu. kawai zamu ce bata zo gidan ba.Gaban Hanan yayi mummunan faduwa. Wai shin waye ma Ashir kuma meye sanaarsa? Wannan tambayar ita ta rinka mata yawo a kanta. Tana tsoron tashi ya sake danneta don zuwa yanzu tasan bayanta ya gama lalacewa.
Kamar masu zuwa sallar idi zulai da Sabuwa duk sababbin kaya suka saka. Dayake akwai kwadayi sam uwale ta manta abinda Ashir yayi mata. Sun riga Sabuwa ma shiryawa. Uwale ko abinci ta kasa ci. Yau dai duk tsiya sai taci abincin gidan Ashir. A daidata sahu suka dauka har gidan. Maigadi da yake bakinsu daya da ubangidan nasa yaso hanasu shiga. Zulai tace haba dan cin arziki ya zaka hanani ganin jikata. Ni fa na haifi uwarta ka ganta ta nuna sabuwa. Uwale ta cangalo yar kafarta ni kuma na haifi ubanta ba. Jin hayaniya tayi yawa yasa Ashir fitowa da kansa. Wani mugun murmushi yayi da ya gansu. Idan yayi cinikinsu ba karamin kudi zai samu ba. Yayi dan murmushi inna sannunku da zuwa. Ku shigo mana. Uwale da zulai har da neman ture juna. Suna shiga falon sai kalle kalle. Sabuwa dadi ya kara kamata yarta tayi dacen mijin kwarai. Hanan da Zaliha ya kira daga sama. Dukkansu a tsorace suka fito. Suna ganin iyayensu zaliha ta karasa saukowa da gudu. Ita kuwa Hanan ta gama tsinkewa da lamarin Ashir tunda taji maganarsa ta waya jiya. Daga bakin benen ya rikota ya hanata sauka. Sabuwa ta saki baki me zan gani ni Sabuwa, Hanan kin ganki kuwa. Duk kin kare kamar kudin guzuri. Kai yaro sako min ita mana. Garin yaya zaliha ta kwana baku sanar da kowa ba. Uwale tace ke kuwa ki bari su sauko mana. Duk kin tsare su da tambaya. Gashi ko karyawa bamuyi ba. Hannan sauko ki bamu abinci kinji yar jikalle.Ashir ya daka musu tsawa ke don Allah ku dakata duk kun isheni da zance. Ke Hanan ki zabi wanda kika fi so cikinsu nayi miki alqawarin babu abinda zai cutar dashi. Sauran kuwa na gama cinikinsu. Zulai tace kai kana da hankali kuwa. Wane irin zance ne wannan? Nancy mai aiki ta fito yallabai sunyi waya fa, idan ta zabi wanda baza a kashe ba zan shiga da ita a dora mata maganin. Zata zama kurma kuma bebeya don haka bazata taba tona maka asiri ba. Sabuwa tace wai Hanan me yake faruwa ne. Ya kalleta yi musu bayani sweety. Ai kamar an kunna rediyo ta sanar dasu komai. Kowa sai kuka da salati. Uwale tace kina nufin Ashiru dan luwadi ne? Tace eh inna da kuma yin kudi da jinin mutane. Meyasa kuka zo? Sabuwa tana kuka tace yanzu wata biyar dinnan a haka kika yi su? Mun shiga uku. Hanan itama kukan take yi...ni kam naga illar son abin duniya. Uwale ta cangala ta rungumo ta. Ba laifin kudi bane Hanan ina jin hannu Dijengala ta sa miki. Wasu garadan maza ne suka shigo gidan su uku. Oga yace ka nuna wadanda zaa dauka. Ai tuni suka saka kuka ana rokonsu. Yace idan bata zabi daya ba shikenan. Gaba dayansu zai kashe. Zulai tace ni na yarda na zama kurmar don Allah ki zabeni Hanan. Uwale tace ni dai idan har kayi alqawarin zaka saketa kuma ka barta tayi rayuwa mai kyau shikenan. Tana kuka tace ni na dorata akan wannan hanyar. Zulai tace kinji ko Hanan ki zabeni. Kema sabuwa zan kular miki da sauram yaranki. Yanzu gwaggo akan kudi kin zabi na mutu. Hanan ta kalle shi Ashir na zabi inna uwale. Sai ta fashe da kuka. Zulai tace sannu inuwar giginya wato ni na mutu ko? To kinyi kadan billahillazi baki isa ba. Nice nan kadai kakarki don babar ubanki ta dade da mutuwa. Sabuwa tayi saurin rufe mata baki yi shiru gwaggo. Barni na fadi son raina kinji ko. Ke uwale Hanan wallahi ba jininki bace. Da cikinta Inuwa ya saki sabuwa. Zaliha ce kawai yar Yakubu to kinji. Haka kawai zaki zabi bare ki bar na gida. Jiri ne ya debi Uwale ta yanke jiki ta fadi.
FARAR HAIHUWA💰42
Hanan duk ta gigice yadda taga Uwale tana shure shure. Ta kalli zaliha ki debo ruwa a shafa mata mana. Zaliha tayi saurin shiga kitchen ta taho da ruwan. Da kyar uwale ta farfado ai kuwa kan Zulai tayi. Yanzu har abin ya kai kiyi irin wannan sharrin. Jinina ki raba ni da shi. Zulai tana kokarin kwace kanta tace Sabuwa ki fadi gaskiya mana. Ya zaki yi shiru kina kallon gurguwar nan zata yi min rauni. Sabuwa wadda ta zauna a kasa tana kuka tace Gwaggo ko Ashiru bai kashemu ba kin riga kin daba mana wuka. Uwale ta kara cakumar Zulai...Allah Ya isa tsakanina dake bazan taba yafe miki ba. Tana kakari saboda taji matsa tace dana yi miki alfarma ko. Yanzu dai kin yarda bakar fata a jininku take tunda gashi yar Yakubu da Sabuwa itama bakar ce. Zaliha da Hanan sai kuka suke yi sosai. Ashir ya dubi kartin dake tsaye...wai me kuke jira ne? Duk a sa min su a mota. Fatana shima uban nasu yazo a kara da nashi kan.
Hajara aminiyar Hanan ta gaji da shirun da take ji daga wurin kawarta. Aure wata biyar amma rabon da su hadu tun ranar da aka kaita. Tana yawan buga wayarta ma bata samu gashi idan tazo gidan sai mai gadi ya tambayi sunanta. Tana cewa Hajara zai ce matar gidan bata nan. Yanzu har ya ganeta. Ita Hajara ta matsu su hadu saboda mutuwar wulakanci da Babba malamin tsibbunsu yayi. A kwata aka tsinci gawarsa. Lamuranta duk sun sukurkuce. Saurayin da take wa asiri sai da akayi da gaske harda hukuma kafin ya kyaleta. Tamkar wani bunsuru ya zame mata. Malamin daya karya asirin yayi mata nasiha sosai shiyasa take son yadda shiriya tazo mata itama Hanan ta samu rabo. Yau da wuri tazo kada tayi rashi saa Hanan ta fita. tana zuwa maigadin ya sakar mata fuska. Hajiyan tana ciki dama ta fada min zaki zo yau...sai wani murmushi yake. Hajara tasan basuyi waya da Hanan ba shiyasa ta dan ja baya. Maigadi na ganin haka baiyi wata wata ba ya fizgota ciki tana ihu. Shima cinikinta zaiyi ya sami rabonsa. Bata dade da soma ihun ba tayi shiru.
Khadija tashi kada ki makara sallah fa. Tayi mika idanunta har yanzu a kumbure ta bude su da kyar. Ta dafe kai, Daddyn Ammar kaina ciwo yake kamar ana sara min guduma. Anya ba fashewa zaiyi ba? Dafa kan yayi tabbas yayi zafi sosai...kinga illar kukan da kika yi min jiya ko? Yar hirar soyayyar ma ta gagara duk irin rarrashinki dana yi. Ta kara kwanciya a jikansa to ai baka iya rarrashin bane. Ya rike baki lallai kinci ganye yarinya. To ni dai ki tashi kiyi sallah zuwa bakwai ki koma baccinki. Zanje wani wuri ne anjima kadan. Ina zaka kuma bayan bani da lafiya ta langabe masa. Hancinta ya ja...ba nisa zanyi ba sai na dawo zan miki bayani.
karfe tara da kwata a layin gidan Ashir tayi wa Sulaiman. Wayar abokinsa tasa yayi parking a gefe yana amsawa. Yana cikin wayar yaga adaidaita ya sauke wata budurwa. Tana cikin magana da maigadi yaga an fizgo ta cikin gidan tana ihu. Abin ya daurewa Sulaiman kai sosai. Yana ta tunani sai ga mota baka mai tint a glass din ta shiga gidan. Amma kafin ta wuce wasu maza ya hango a ciki. Zuciyarsa babu abinda bata kitsa masa. Ya sake kiran Sakina a waya ta tabbatar masa gidan da yake hange shine na Ashir. Har yazo kofar gate din ya tuna da Azkar din safe da baiyi ba..yayi adduarsa sai kawai yaji zuciyarsa bata aminta da ya shiga ba. Office din 'yan sanda mafi kusa yaje ya nemi a taimaka masa kanwarsa ce wani ya sace. Yadda yayi niyya a ransa idan har ba cutar wannan yarinyar zaayi ba sai kawai ya wayance yace kama tayi da kanwarsa.
Dukkansu aka jere a bakin motar an daure musu idanu, baki da hannuwa. Ruwan hawaye kawai suke yi. Hanan ta durkusa gaban Ashir tana ta magiya ko a jikinsa. Karshe ma cewa yayi idan an sami kudin fa ni dake zamu ci da dan jaririna. Mamaki ne ya kara kamata lokacin da taga maigadi yana jan Hajara kamar tunkiya a kasa. Yace yallabai nima ga nawa kamun ayi mata kudi. Hanan ta tashi da gudu zata je ta riketa tana kiran sunanta Ashir yasa kafa ya tadeta ta fadi kasa. Wani ihu ta fasa don akan cikinta wanda ya fara fitowa ta fadi.
Sulaiman yace da yan sandan kunji abinda nake fada muku ko. Daya daga cikin mazan yace Ashir kana son matarka ta tara mana jamaa ne? Idan bata yi shiru ba zan hada da ita. Bugu suka ji a bakin gate...maigadi yayi dariya yallabai ga wani naman ya iso. An fara loda su Uwale a mota kamar kayan wanki maigadin ya bude karamar kofar gate. Bindiga ya gani a saitin goshinsa yayi saurin yin baya. Yan sanda sunfi goma suka shigo gidan tare da Sulaiman. Sai gudu mazan zasu tsere, shima Ashir hanyar shiga gidansa yayi da gudu. Yan sanda suka bude wuta sai da suka harbi mutum biyu daya a kafa daya a kafada. Sauran duk suka nutsu. Ashir ya rasa inda zaiyi...yana kokarin shiga gida wani dan sanda yana cewa stop! Stop!! Ganin bai tsaya ba ya harbe masa cinya. Sannan aka hada su akayi waje dasu.
Sulaiman da taimakon wani dan sanda suka kwance su Uwale. Saboda idonta ya dade a rufe bata gani sosai tace har mun zo lahira ne? Wayyo ni ko kalmar shahadar ma ban sami yi ba. Kasa ta durkusa da yar kafarta tace Allah, Allah , Allah na tuba Ya Allah. Ina tsoron wuta dama na zata zan sami lokacin tuba ne. Sulaiman yace Inna bude idonki da kyau nine sulaiman. Ta kara sa kuka ayya ashe kaima Ashirun ya kashe ka. Allah Sarki Dije da Munari ban sami damar rokonsu gafara ba. Zulai tace ke banza bamu mutu ba fa. Ai ni na debo da yawa. Uwale na jin muryar zulai tace shikenan nima wutar za a sani...na shiga uku ai tunda muka sake haduwa a lahira zulai nasan tawa ta kare. Wani wawan mari taji wanda yasa ta dena sumbatu...zulai ce da wannan aikin. Uwale na bude idonta da kyau taga Sulaiman. Rungumarsa tayi kamar uwa taga jaririnta daya bata ta dan albarka nagode..
FARAR HAIHUWA💰43
Ashir da dukkan jamaar gidansa aka kwashe su a mota. Zaliha tayi karfin cewa yallabai akwai mace a ciki. Nancy a cikin toilet ta buya tunda taji harbi...amma bata tsira ba don kuwa sai da suka binciko ta.
Zaliha ta kamawa Sulaiman suka saka Hanan a mota. Dukkansu asibiti suka nufa aka ajiye wasu yan sandan da wadanda aka harba. Sauran kuma aka wuce dasu police station. Sulaiman ya kira Mal Yakubu, ummansa da mahaifin sakina tunda kanin baban Ashir ne. Cikin kankanin lokaci asibitin ya cika da mutanen da abin ya shafa. Dakin theatre aka shigar da Hanan saboda yadda take zubar da jini. Duk suna zaune jugum jugum har aka fito da ita. Sabuwa tayi ta addua a ranta Allah Yasa cikin ya zube, me zasu yi da jinin Ashir. Sai bayan awa daya da yan mintuna aka fito da Hanan. Ana turata daki likita ya bukaci ganin iyayenta. Dakin suka shiga Uwale har da cewa Umma kema ai babarta ce ki shigo. Ina Sulaiman dan albarka. Yace inna gani tace ku taho mana. Ai wannan abin ya shafi kowa. Kema mahaifiyar Ashiru kinfi kowa cancanta da jin komai. Likita ya dube su yadda suka cika dakin yace lallai Hanan Yaqub kina da dangi, kin zama yar gata tayi wani murmushin bakin ciki..sannan ya cigaba da bayani yana kallon Mal Yakubu. Na riga na sanar da ita komai, amma kana ganin dukkan mutanen nan ya kamata su ji komai? Mal Yakubu yace kayi bayaninka kawai likita ba damuwa. Ya numfasa to a gaskiya Hanan tana da hawan jini domin har ya taba zuciyarta. Zulai ta katse shi ni ba wannan ba ya batun cikin? Uwale ta wani harareta. Likita ya shareta ya cigaba da magana. tana bukatar hutu da nutsuwar zuciya sosai, cikin jikinta bai tabu ba sai dai dole zamu bata bed rest wato hutu har ta haihu. Abu na gaba shine bazamu bari ta haihu da kanta ba saboda taji ciwo sosai a bayanta. Aiki zamu yi mata. Mal Yakubu cikin rashin fahimta yace me ya sami bayan? Likita ya sunkuyar da kansa. Mijin Hanan yana nemanta ta baya ne don a halin yanzu ya kamu da infection a wurin sai munyi maganinsa har ruwa yake yi. To ina ganin haihuwar zata zo kafin ta warke tunda cikin yayi wata biyar. Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun. Kowa ya na ta salati su Dije harda kuka. Haj Lami maman Ashir tace cikin kuka sharri zakuyi masa don kunga baya nan? Likita yace yana nan mana ana cire masa bullet daga cinyarsa ne. Ta zaro idanu ta kalli baban Sakina. Mun shiga uku Alhaji kaga zasu kashe min da. Zulai tace dole ki fadi haka mana tunda kin haifawa duniya masifa. Nan dai suka hadu har da yan sandan dake gadin su Ashir aka sanar da kowa abinda ke faruwa. Tamkar anyi rashi haka suka rinka kuka. Musamman da Hanan ta fadi irin zaman data yi. Mal Yakubu yana zubar da hawaye ya matsa zai zauna bakin gadon ya rarrasheta Uwale ta daka masa tsawa. Sabuwa na jin haka tasha jinin jikinta. Uwale tace dawo nan munafuka. Dan nan ko kasan Hanan ba yarka bace? Ashe bayan an saketa da kwana biyar aka daura muku aure ba iddah ga ciki wata biyu. Subhanallah!!! Kawunan su duk sun daure saboda kaduwa da jin zancen. Mal yakubu ya kalli Sabuwa, Allah zai mana sakayya ni da ke da mahaifiyarki. Ya kalli Zaliha ita wannan tawa ce ko kuwa? Tana rawar jiki tace wallahi mal yarka ce. To ni dai ban ma san hukuncin aurenmu na amma na sakeki saki uku. Uwale ta rangada guda Allah Yayi maka albarka. Ta kalli Zulai sai ku kwashe kayanku a kara gaba. Mak Yakubu yace dukkanmu zamu tashi ai gidan wannan dan iskan ne. Hanan tayi kuka sosai. Khadija da Zaliha suna ta rarrashinta. Mal Yakubu yace bazan taba kyamarki ba domin ke yar aure ce kamar kowa. Itama zaliha yar aure ce tunda an sake sabuwa amma hakkin mijinta ne tayi masa idda kafin wani ya aureta. Ki koma ki nemi gafarar tsohon mijinki da Allah SWT. Hanan tace to Baba ni meye makomata? Yadda tayi maganar abi tausayi yace da kaina zan kaiki wurin mahaifinki domin yasan gaskiya amma zan roke shi alfarma ya bar min ke. Tana zubar da hawaye tace nagode baba Allah Ya saka maka da alkhairi. Sannan tayi musu bayanin asirin da tayiwa Ashir. Ku tayani adduar neman gafarar Allah ko da mutuwa zata riskeni.
Mahaifiyar Ashir ko dakin d yake taki shiga tunda taji irin sabon da yake aikatawa. Cewa tayi ko a lahira bata fata sake ganinsa. Ta dubi Baban sakina ,kaga da yake bata da hakki Allah Ya kiyayeta har ta sami wani mijin. Tana gama magana ta fice.
A wannan ranar su Mal Yakubu suka tashi suka koma tsohon layinsu. Gidan Gwaggo suka nemi alfarma su zauna kafin ya gama gyaran gidansa. Ba yadda Sulaiman baiyi ba su tafi tare Mal Yakubu yaki. Haka Zaliha da khadija suka rinka jinyar Hanan. Itama Uwale da ta leqa lahira ta dawo ta saduda. Ta amsa laifinta na kara batawa Hanan tarbiya shiyasa bata guje ta ba tunda abin ya faru. Mal Inuwa da sauran 'ya'yansu har asibitin sun zo. Shima dai yace bazai yafewa su Zulai ba kuma yana fata Hanan zata rinka zuwa wurinsa a kauye tunda yasan har abada ita yar Mal Yakubu ce.
FARAR HAIHUWA💰44
Bayan Hanan tayi sati biyu jikinta ya danyi sauki 'yan sanda suka bukaci ta zo domin tayi cikakken bayani akansa. Tare da iyayenta maza biyu suka je da Uwale. Nasa iyayen duk sun zame hannunsu akansa. Da kyar yake tafiya saboda tadda cinyarsa wurin da aka cire bullet yaki hadewa. Kafar ta kumbura suntum tana wari. Suna tsaye mal Inuwa yace cakumi wuyansa yana cewa ya sakar masa 'ya. Ashir yayi wani murmushi ai ni da ita mutu ka raba. Sai dai tayi min takaba. Mal Inuwa yace kai ni fa wallahi dan tasha ne in fada maka. Sai na karasa ka idan yaso a kulleni. Mal yakubu yace kayi hakuri a gaban hukuma muke fa. yan sanda suka shiga tsakani sai ga wani dan dattijo ya shigo da wani yaro kyakkyawa. Suna tsoho rai a bace yace ,kara ya kawo makocinsu ya bata masa jiķa. Yaron nan maraya ne ga kokari a makaranta. Lokaci guda ya zama fitsararre mara kunya.shine na tsananta bincike ya fada min har makaranta mutumin yake binsa. Wani dan sanda yace Baba dan dakata ka huta sai kayi bayani cikin nutsuwa. Wace nutsuwa kuma dan sanda? Kaga fa duburarsa ta kusa burmawa ga wani ruwa mai doyi. Wallahi kakarsa har suma tayi jiya. Hanan ta karewa yaron kallo ai shine wanda ta kama Ashir da shi. Yaron idanun sa ko gezau ya ga Ashir yace ai ga saurayin nawa. Kakansa ya kunduma masa zagi yallabai kun gani ko? Ko rissina baiyi ba. Dan sanda yace kai kam Ashir ka gama yawo laifinka yayi yawa. Zamu shiga kotu ranar litinin idan baka saki matar taka a nan ba alkali zai raba. Mal Yakubu yace da kakan yaron kaga ka kai shi asibiti a nema masa magani sai ka nemi makarantar yara marasa ji a saka shi domin a gyara tarbiyarsa.
Umma tasa Sulaiman ya nemarwa Mal Yakubu wani gidan amma sam yace bazai shiga ba. Aikin da aka bashi ya ishe shi. Da kansa da taimakon abokansa yake gyaran tsohon gidansu. Gwaggo ba karamin taimako take masa ba da iyalinsa.
Watanni biyu da faruwar wannan al'amari Khadija ta gama ajin mata a Muslimah Institute. Ta koyi gyaran jiki, hada humra da turaren wuta, gyaran gida da girke girke kala kala. Duk juma'a Sulaiman yana kaita gidansu ta yini idan ya taso aiki yazo daukarta. Uwale tamkar ta lashe Khadija da mijinta. Bata gajiya da rokonta tayi hakuri. Sulaiman yace idan anyi musu walima da bada certificate daga makaranta zai kaisu garinsu a nemi Munari.
Wani hadadden lace Khadija ta saka. Jikinta duk ya ciko da kara kyau. Tana saka sarka Sulaiman yayi hugging dinta ta baya yana shakar kamshin jikinta. Khadija duk kin canja ko dai...ya dan shafa cikinta. Tayi dariya ko dai me? Ina ganin kamar akwai dan saurayi ko budurwa a cikin nan. Ta sunkuyar da kai tana murmushi...ya rike baki yanzu shine baki fada min ba, Wata nawa ne? Bata bashi amsa ba ta fice daga dakin tana dariya. Ita kanta bata san ko wata nawa bane kila dai yakai uku. Umma ce ta fara ganewa tace mata ta dena hawa sama da gudu saboda jikinta. Tace Umma ai ance motsa jiki yana da kyau...ita bata gane abinda surukar tata take nufi ba. Umma tace ai ko dai idan yayi yawa irin wanda kike yi yana sa mace tayi bari. Ta zaro ido bari kuma umma? Ai Daddyn Ammar yafa cin abinci a kasa ma. Kuma fa wallahi sai na rike tray sosai nake hawa dashi. Zan dai fada masa a hakura da cin abincin a sama. Haka kawai naje na fadi naji ciwo. Umma duk yadda taso daurewa sai da tayi dariya. Tace khadija baki yi gwajin ciki bane? Nan tasa Khadija jin kunya.
Hijab dinta da takalmi ya biyota dasu falon . Umma sa Ammar duk sun shirya zasu walimar makarantarsu Khadija. Iyalin gidan Mal Yakubu da Gwaggo suma daga hotoro Sulaiman yayi musu kwatancen makarantar.
FARAR HAIHUWA💰45
Harabar makarantar cike take da motocin alfarma. Duk bayan wata shida ake yin walimar dalibai daga ajujuwa daban daban. Masu karatun boko da islamiya ne kadai suke yin shekara uku. A wannan bangaren Khadija da sauran karatu. Iya zamanta Allah baisa sun taba haduwa da mai makarantar ba. So take tayi mata godiya bisa wannan taimako da take yiwa 'ya'ya mata. Su Inna ta hango ana cangala kafa tasha leshi. Hanan ciki ya soma nauyi da kyar take takawa amma ta nace sai tazo. Zaliha kuwa da gudu tazo ta rungume Khadija. Sulaiman yace kinga kiyi mata a hankali bana son ganganci. A hankali kuma Yaya Sulaiman? Ta dan dag gira ko dai abin yazo? Dundu khadija tayi mata don tasan Uwale tana jinsu. Ai kuwa uwalen tace yara zaku sha ruwan zafi indai ba samari kuka haifa ba.
An nunawa baki wurin zamansu. Dalibai masu fita kowacce suna bangarensu. Yan ajin dinki sunsa farin hijab har kasa, su Khadija maroon sai masu saka brown. Yawancinsu duk masu aure ne. Manyan baki suna daga gefe daya. Bangaren maza daban na mata daban. An bude taro da addua , Sadisu Yaqub shine a matsayin mai gabatarwa.
Manyan bakin yawanci manyan yan kasuwa ne dama aikatan gwamnati. Bayan jawabi daga babban bako na musamman sai aka kira shugaban AmJu Airlines wato Rayyan mijin Amal da Juwairiyya (Ju) wanda yayi alqawarin kujerun makka ga dukkan dalibai da suka yi ukun farko a kowanne bangare. Nan da nan wurin ya kaure da kabbara. Daga nan aka kira Alh Salihu Ado wanda yayi fice a harkar siyasa da kasuwanci. Yana fara magana gaban Mal Yakubu da Uwale dake can gefen mata ya fadi. Tabbas Yaya Salihu ne yayan matarsa. Hanan tayi yunkurin tashi Zaliha tace ina zaki? Tace matar nan data taimaka min a asibiti wadda nake baku labari ita na hango. Uwale bata ma ji abinda hanan ta fada na don hankalinta sam baya tare da ita. Shima Alh Salihu yace ya bada dubu hamsin ga dukkan wadanda suka yi na ukun farko. Su Khadija sai murna.
Hanan ta sameta suka gaisa. Da farko ma bata ganeta ba saboda ciki ya sa ta kara kiba. Tace 'yata ya jikinki ya maigidan? Hanan tace mata Haj idan an gama taron nan zan miki bayani. zata sake magana aka fara kiran sunayen ukun farko a kowanne aji. Hanan tace bari na koma Allah Yasa a kira kanwata. Ai kuwa tana zama aka kira ta biyu daga ajin gyaran jiki da girki.... Khadija Yakubu murna a wurin Dijengala baa magana. Ta mike da sauri ta kallo wurin da su Inna suke. Suma daga mata hannu sukayi. Ta kallo Sulaiman yayi motsi da bakinsa wanda ta gane I love you yace.shi kuwa mal Yakubu burinsa ayi a gama taron ya sami ganin Yaya Salihu. Ammar ya baro wurinsu da gudu yana ihun Mommy.
Bayan an gama ne aka bukaci uwar taro tazo ta rufe wurin da addua da godiya. Sadisu yace mai masaukin baki muna bukatar ki fito kiyi godiya ga dukkan wadanda suka sami halartar taron nan...Haj Maimunatu Ado.
FARAR HAIHUWA💰46
Cikin nutsuwa ta tashi ta nufi wurin da Sadi yake tsaye yana mata murmushi. Matan dake wurin suka rinka cewa Maama suna murnar ganinta. Sunanta kenan har a makarantar. Tana karbar mic din tace Assalam Alaikum....sai ji suka yi cikin daga murya ance La ila ha illallahu MUNARI????
Gabanta ne ya fadi sosai...kamar muryar Inna Uwale. Mal Yakubu ya kusa isa inda take tsaye. Inna Uwale ma ta kusa faduwa daga kujerar da take zaune saboda saurin da take yi ta tashi. Su ukun duka kuka suke yi. Tani da sauran yan uwanta duk sun gane su. Munari muryarta har rawa take yi amma bata ajiye loudspeaker din ba. Tace Inna? Malam?
Mal Yakubu wurin da khadija take zaune yaje ya janyo hannunta. Haka ta bishi suka karasa Munari tana kallonsu tana kuka jamaa kowa yana tunanin me yake faruwa. Suna tsayawa gabanta Mal Yakubu ya kama hannun Khadija yace Alhamdulillah Dije ga mahaifiyarki.
Sulaiman saurin tasowa yayi ya karasa wurin domin kowa yaji abinda ya fada. Salati da kabbara kawai ake yi. Munari ta daga hannu ta shafa fuskar Khadija wadda ta gama jikewa da hawaye. Rungume juna suka yi sosai suna kuka. Muryar Munari tana ta kuwwa tana cewa Allahu Akbar. Sadi ya sauko shima ya tsaya gefen su. Munari bata saki Khadija ba tace masa ga mahaifinka Sadi, ga kanwarka. Allah Ya amsa adduarmu.
Uwale ta samu ta durkusa gaban Munari tana rokon gafara. Tayi saurin dagata suka rike juna haba Inna don Allah ki bar wannan maganar. Haduwar mu a nan ya ishemu godiya ga Allah. Kuzo mu shiga ciki. Uwale tace bani abin maganar nan don girman Allah. Ba musu ta mika mata.
Jama'a assalamma alekun. Nasan kowa yana mamakin abinda yake faruwa a wurin nan. Ta nuna munari, shekaru goma sha takwas kenan dana sa dana ya saketa babu gaira babu dalili. Na takura mata, na cutar da ita. Nayi sanadin mutuwar yarta ma amma bata taba daga min murya ba. Ta cigaba da kyautata min. Ni kuma na dora mata karan tsana...Uwale haka ta rinka bayanin rayuwarsu da irin yadda ta rike Dije. A karshe tace hakika farar haihuwa ba a haihuwar da fari mai kyau bace. Kowanne da da arzikinsa yake zuwa. Duk abinda Allah Ya bamu don Allah mu karba da godiya da farin ciki. Arziki da talauci duk na Allah ne. Ku tayani rokon yaran nan su yafe min. Na zamewa dana alaqaqai saboda bakin hali. Gashi yau arzikin bakaken muke ci gaba dayanmu. Kyau da muni ba sune mutum ba. Zuciya da albarka daga Allah SWT shine abin nema daga Allah. Nagode
Mata har da wasu mazan sai kuka sukeyi. Rayuwar su Uwale ta zame musu wata ishara a rayuwa. A gaggauce aka rufe taro suka tafi gidan Haj Maimunatu. Bakin Uwale a bude tace yanzu munari nan gidanki ne? Kina da miji ne? Murmushi kawai tayi suka shiga gidan
Gida kam babba ne kuma mai kyau. Sun hadu da Inno da Inna Ladi.Suka zauna aka gabatar musu da su Umma da Gwaggo. Maama wato munari tace ai Haj Bintu kawata ce Allah baisa na taba ganin surukarta bane. Ta kalli Sulaiman tace Allah Yayi maka albarka. Hanan tace ai ita ce matar da nake fada muku Baba. Munari ta taya su bakin cikin abinda ya faru dasu sosai. Hira dai har dare ranar. Khadija duk inda mahaifitarta rasa kafa tana biye da ita. Sadi ya bada labarin lokacin da suka fara haduwa. Matar Alh Salihu tace dama ita ce kurmar da ka bamu labari. Kowa sai dariya da suka rinka jin shirmen da take yi da. Munari ta basu labarin auren data yi da kuma rasuwar mijin. Inda tayi amfani da gadonta wurin fara makarantar da taimakon yayanta. Dare nayi suka fara tafiya...Umma tace wa Sulaiman zaka bar Khadija anan ta kwana biyu ko? Yace ai dole ne Umma. Maama tace idan ma yaki sai na basu daki.
Haka suka kasance cikin farinciki. Bayan sati biyu aka yiwa Hanan aiki aka ciro mata danta. Dr Auwal shine likitan da yake dubata tun farko kuma shi yayi mata aikin. Bayan an ciro dan ya rike shi yana kallon Hanan yace kinga munyi kama dashi. Ina fata zaki yarda ya kirani Baba. Hawaye ne ya zubo mata data tuna waye ainihin babansa. Dama an raba aurensu bayan kotu ta yanke masa daurin rai. Yan uwan Hanan na bangaren babanta duk sun zo. Zulai da Sabuwa ma sunzo dubata. Da kyar aka samu ta yafe musu. Iyayen Ashir kuwa sunyi mata sha tara ta arziki. Domin sunce suna son jikansu. Hatta Sakina da mijinta sunzo.
Yaqub ta zaba a matsayin sunan danta. Suna kiranshi Abba. Dr Auwal kuwa da gaske yake yana son ta amince ya aureta. Zaliha ma an soma daidaitawa da Ali babban dan Alh Salihu.
A ranar sunan ne Munari ta samu yin magana da Mal Yakubu. Baya taba bari su kebe. A soro ta hadu dashi zata fita suka gaisa yana sauri zai wuce. Tace Mal Yakubu zance fa nazo wurinka....har tuntube yayi saboda mamakin abinda ta fada. Zan..zan me? Tace zance mana. Wane iri ya fada cikin rashin fahimta. Tace na neman aure mana. Ya kalleta har yanzu yana matukar sonta amma wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa. Haj Maimuna ba Munarinsa ta qauye bace. Itama tasan meyasa yake gudunta shiyasa ta zabi yin magana. Maimunatu ina zan kaiki? Inda ka kaini da Malam. Kinga gidan da nake ciki fa? Nawa gidan da duk arzikin dana yi namu ne mal. Ban taba dena sonka ba.
Satin daya zagayo aka daura musu aure. Uwale tana ta kukan farinciki. Ga shi sun koma gida mai kyau. Gwaggo ta zama yar gida itama. Su Khadija suna kyautata mata sosai.
Rayuwarsu abin shaawa ga kowa kuma darasi ga mai fahimta. Bayan wata shida Khadija ta haifi 'ya mace. Sulaiman kamar wani ango don murna. Umma da kanta take yiwa jaririya wanka. Ranar sunanta ga mamakin kowa yarinya taci suna Ramlah. Munari sai da tayi kuka don murna. Tana ta sa musu albarka. Sadi yace to maama tunda kika ga wannan yar ni kuma kin sani a gefe. Dundu yaji mai zafi daga wurin Khadija. Yace kai kai kai sai na rama. Haba Sadi haihuwa fa tayi Maama ta fada tana saurim tarewa. Umma tace eh lallai maganarka ta fito dana. Sulaiman ya kalli Ammar da ya rungume baby yace indai tsokana ce to Dijengala ta zarce kowa. Filo ta jefa masa tana tura baki. Umma kin ganshi ko. Uwale tace kyale su zan rama miki.
HAMDAN KATHIRAN DAYYIBAN MUBARAKAN FIH.
TAKU
Batul Mamman💖
Lovely. Allah ya qara basira *meemee_beee*
ReplyDeleteIna Amanda KARIPETRA zaune a USA, i sun a fama da herpes, domin shekaru masu yawa, tsawon 7years, ba tare da magani. a kan daya aminci rana i ga wani labarin a kan internet aka mace yi magana game da likita ISE kuma yadda wannan likita warke ta har abada daga cutar HIV / AIDs.I gaya masa na rashin lafiya. Wannan grate mutum warke ta herpes kamuwa da cuta cutar. Ya aiko ni ganye magani wanda ya warkar da ni gaba daya .Email shi @ ISESPIRITUALSPELLTEMPLE@GMAIL.COM ... Yau I`m rai da farin ciki da kuma free daga herpes. Ina da gama kan tuna cewa babu wani magani, shi ne mai shi da kuma kafa ISE ganye BINCIKE Centre [IHRC] Dr .ISE sun magani domin HIV, Zika, HPV, fuka, ciwon sukari, syphilis, low maniyyi count, da ciwon daji , hauka, hepatitis, kwayoyin da parasitic kamuwa da cuta da kuma sauran related kwayar cutar. Yana da kashe 15 shekara ta a aikatawa spiritualism, tuntuba, ta yin amfani da ganye da kuma ruhaniya wajen warkar da rashin lafiya a duk faɗin duniya. Babban dalilin da nake rubuto wannan shaida ne sanar da dukan duniya game da manyan ayyuka, kuma shĩ ne mai ganye Doctor wanda zai iya warkar da m cututtuka. Shi ne kuma mai girma sihiri Caster ina da ba ga wani Doctor haka m kamar wannan grate mutum, ya na da ajiye yawa rayuwa. Za ka iya tuntuɓar shi via; ISESPIRITUALSPELLTEMPLE@GMAIL.COM ... 0r +1954621192
DeleteIna Amanda KARIPETRA zaune a USA, i sun a fama da herpes, domin shekaru masu yawa, tsawon 7years, ba tare da magani. a kan daya aminci rana i ga wani labarin a kan internet aka mace yi magana game da likita ISE kuma yadda wannan likita warke ta har abada daga cutar HIV / AIDs.I gaya masa na rashin lafiya. Wannan grate mutum warke ta herpes kamuwa da cuta cutar. Ya aiko ni ganye magani wanda ya warkar da ni gaba daya .Email shi @ ISESPIRITUALSPELLTEMPLE@GMAIL.COM ... Yau I`m rai da farin ciki da kuma free daga herpes. Ina da gama kan tuna cewa babu wani magani, shi ne mai shi da kuma kafa ISE ganye BINCIKE Centre [IHRC] Dr .ISE sun magani domin HIV, Zika, HPV, fuka, ciwon sukari, syphilis, low maniyyi count, da ciwon daji , hauka, hepatitis, kwayoyin da parasitic kamuwa da cuta da kuma sauran related kwayar cutar. Yana da kashe 15 shekara ta a aikatawa spiritualism, tuntuba, ta yin amfani da ganye da kuma ruhaniya wajen warkar da rashin lafiya a duk faɗin duniya. Babban dalilin da nake rubuto wannan shaida ne sanar da dukan duniya game da manyan ayyuka, kuma shĩ ne mai ganye Doctor wanda zai iya warkar da m cututtuka. Shi ne kuma mai girma sihiri Caster ina da ba ga wani Doctor haka m kamar wannan grate mutum, ya na da ajiye yawa rayuwa. Za ka iya tuntuɓar shi via; ISESPIRITUALSPELLTEMPLE@GMAIL.COM ... 0r +1954621192
DeleteEnter your comment...Thanks a lot sis Batul...Allah qara basira😘
ReplyDeleteAllah ya kara basira, ya saka da mafificin Alheri.
ReplyDelete"I like this post,And I guess that they having fun to read this post,they shall take a good site to make a information,thanks for sharing it to me.
ReplyDeleteRead more here:
kim kardashian sex tape
porn sex video hd
mia khalifa sex video
sunny leone sexy movie"